< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job answered and said,
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Of a truth I know that it is so: but how can man be just with God?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
If he be pleased to contend with him, he cannot answer him one of a thousand.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
[He is] wise in heart, and mighty in strength: who hath hardened himself against him, and prospered?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Which removeth the mountains, and they know it not, when he overturneth them in his anger.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Which shaketh the earth out of her place, and the pillars thereof tremble.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Which commandeth the sun, and it riseth not; and sealeth up the stars.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Which alone stretcheth out the heavens, and treadeth upon the waves of the sea.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Which maketh the Bear, Orion, and the Pleiades, and the chambers of the south.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Which doeth great things past finding out; yea, marvelous things without number.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Lo, he goeth by me, and I see him not: he passeth on also, but I perceive him not.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Behold, he seizeth [the prey], who can hinder him? who will say unto him, What doest thou?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
God will not withdraw his anger; the helpers of Rahab do stoop under him.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
How much less shall I answer him, and choose out my words [to reason] with him?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Whom, though I were righteous, yet would I not answer; I would make supplication to mine adversary.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
If I had called, and he had answered me; yet would I not believe that he hearkened unto my voice.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
For he breaketh me with a tempest, and multiplieth my wounds without cause.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
He will not suffer me to take my breath, but filleth me with bitterness.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
If [we speak] of the strength of the mighty, lo, [he is there]! and if of judgment, who will appoint me a time?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Though I be righteous, mine own mouth shall condemn me: though I be perfect, it shall prove me perverse.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
I am perfect; I regard not myself; I despise my life.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
It is all one; therefore I say, He destroyeth the perfect and the wicked.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
If the scourge slay suddenly, he will mock at the trial of the innocent.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
The earth is given into the hand of the wicked: he covereth the faces of the judges thereof; if [it be] not [he], who then is it?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Now my days are swifter than a post: they flee away, they see no good.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
They are passed away as the swift ships: as the eagle that swoopeth on the prey.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
If I say, I will forget my complaint, I will put off my [sad] countenance, and be of good cheer:
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
I am afraid of all my sorrows, I know that thou wilt not hold me innocent.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
I shall be condemned; why then do I labour in vain?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
If I wash myself with snow water, and make my hands never so clean;
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Yet wilt thou plunge me in the ditch, and mine own clothes shall abhor me.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
For he is not a man, as I am, that I should answer him, that we should come together in judgment.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
There is no daysman betwixt us, that might lay his hand upon us both.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Let him take his rod away from me, and let not his terror make me afraid:
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Then would I speak, and not fear him; for I am not so in myself.

< Ayuba 9 >