< Ayuba 8 >
1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
І заговорив шух'я́нин Білда́д та й сказав:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
„Аж доки ти бу́деш таке тереве́нити? І доки слова́ твоїх уст будуть вітром бурхли́вим?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Чи Бог скри́влює суд, і хіба Всемогу́тній викри́влює правду?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Якщо твої діти згріши́ли Йому, то Він їх віддав в руку їх беззако́ння!
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Якщо ти зверта́тися будеш до Бога, і бу́деш блага́ти Всемогу́тнього,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
якщо чистий ти та безневи́нний, — то тепер Він тобі Свою милість пробу́дить, і напо́внить оселю твою справедли́вістю,
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
і хоч твій поча́ток нужде́нний, але́ твій кінець буде ве́льми великий!
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Поспитай в покоління давні́шого, і міцно збагни́ батьків їхніх, —
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
бо ми ж учора́шні, й нічо́го не знаєм, бо тінь — наші дні на землі, —
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
отож вони на́вчать тебе, тобі скажуть, і з серця свойо́го слова́ подаду́ть:
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Чи папі́рус росте без болота? Чи росте очере́т без води?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Він іще в доспіва́нні своїм, не зривається, але сохне раніш за всіля́ку траву:
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
отакі то доро́ги всіх тих, хто забува́є про Бога! І згине надія безбожного,
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
бо його споді́вання — як те павути́ння, і як дім павукі́в — його певність
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
На свій дім опира́ється, та не встоїть, тримається міцно за ньо́го, — й не вде́ржиться він.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Він зеленіє на сонці, й галу́зки його випина́ються понад садка́ його, —
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
на купі каміння сплело́ся коріння його, воно між камі́ння вросло́:
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Якщо вирвуть його з його місця, то зречеться його́: тебе я не бачило!
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Така радість дороги його, а з по́роху інші ростуть.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Тож невинного Бог не цурається, і не буде тримати за ру́ку злочи́нців,
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
аж напо́внить уста́ твої сміхом, а губи твої — криком радости...
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Твої ненави́сники в сором зодя́гнуться, і намету безбожних не буде!“