< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Kisha Bildadi Mshuhi akajibu:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
“Hata lini wewe utasema mambo kama haya? Maneno yako ni kama upepo mkuu.
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Je, Mungu hupotosha hukumu? Je, Mwenyezi hupotosha kile kilicho haki?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Watoto wako walipomtenda dhambi, aliwapa adhabu ya dhambi yao.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Lakini ukimtafuta Mungu, nawe ukamsihi Mwenyezi,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
ikiwa wewe ni safi na mnyofu, hata sasa atainuka mwenyewe kwa niaba yako, na kukurudisha katika mahali pako pa haki.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Ijapokuwa mwanzo wako ulikuwa mdogo, lakini mwisho wako utakuwa wa mafanikio.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
“Ukaulize vizazi vilivyotangulia na uone baba zao walijifunza nini,
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
kwa kuwa sisi tumezaliwa jana tu na hatujui lolote, nazo siku zetu duniani ni kama kivuli tu.
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Je, hawatakufundisha na kukueleza? Je, hawataleta maneno kutoka kwenye kufahamu kwao?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Je, mafunjo yaweza kumea mahali pasipo na matope? Matete yaweza kustawi bila maji?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Wakati bado yanaendelea kukua kabla ya kukatwa, hunyauka haraka kuliko majani mengine.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Huu ndio mwisho wa watu wote wanaomsahau Mungu; vivyo hivyo matumaini ya wasiomjali Mungu huangamia.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Lile analolitumainia huvunjika upesi; lile analolitegemea ni utando wa buibui.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Huutegemea utando wake, lakini hausimami; huungʼangʼania, lakini haudumu.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Yeye ni kama mti ulionyeshewa vizuri wakati wa jua, ukieneza machipukizi yake bustanini;
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
huifunganisha mizizi yake kwenye lundo la mawe, na kutafuta nafasi katikati ya mawe.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Unapongʼolewa kutoka mahali pake, ndipo mahali pale huukana na kusema, ‘Mimi kamwe sikukuona.’
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Hakika uhai wake hunyauka, na kutoka udongoni mimea mingine huota.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
“Hakika Mungu hamkatai mtu asiye na hatia, wala kuitia nguvu mikono ya mtenda mabaya.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Bado atakijaza kinywa chako na kicheko, na midomo yako na kelele za shangwe.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Adui zako watavikwa aibu, nazo hema za waovu hazitakuwepo tena.”

< Ayuba 8 >