< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Y respondió Baldad Sujita, y dijo:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
¿Hasta cuándo hablarás esto, y las palabras de tu boca serán como un viento fuerte?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
¿Si pervertirá Dios el derecho, y si el Todopoderoso pervertirá la justicia?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Si tus hijos pecaron contra él, él los echó en el lugar de su pecado.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Si tú de mañana buscares a Dios, y rogares al Todopoderoso:
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
Si fueres limpio y derecho, cierto luego se despertará sobre ti, y hará próspera la morada de tu justicia:
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
De tal manera que tu principio habrá sido pequeño en comparación del grande crecimiento de tu postrimería.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Porque pregunta ahora a la edad pasada, y dispónte para inquirir de sus padres de ellos;
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
Porque nosotros somos desde ayer, no sabemos, siendo nuestros días sobre la tierra como sombra.
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
¿No te enseñarán ellos, te dirán, y de su corazón sacarán estas palabras?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
¿El junco crece sin cieno? ¿crece el prado sin agua?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
¿Aun él en su verdura no será cortado, y antes de toda yerba se secará?
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Tales son los caminos de todos los que olvidan a Dios; y la esperanza del impío perecerá.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Porque su esperanza será cortada, y su confianza es casa de araña.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
El estribará sobre su casa, mas no permanecerá en pie: recostarse ha sobre ella, mas no se afirmará.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Un árbol está verde delante del sol, y sus renuevos salen sobre su huerto:
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
Junto a una fuente sus raíces se van entretejiendo, y enlazándose hasta un lugar pedregoso.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Si le arrancaren de su lugar, y negare de él, diciendo: Nunca te vi:
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Ciertamente este será el gozo de su camino; y de la tierra de donde se traspusiére retoñecerán otros.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
He aquí, Dios no aborrece al perfecto, ni toma la mano de los malignos.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Aun henchirá tu boca de risa, y tus labios de jubilación.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Los que te aborrecen, serán vestidos de confusión; y la habitación de los impíos perecerá.

< Ayuba 8 >