< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Potem je odgovoril Bildád Suhéjec in rekel:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
»Doklej boš govoril te stvari? In kako dolgo bodo besede iz tvojih ust podobne močnemu vetru?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Mar Bog izkrivlja sodbo? Mar Vsemogočni izkrivlja pravico?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Če so tvoji otroci grešili zoper njega in jih je zavrgel zaradi njihovega prestopka,
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
če hočeš zgodaj iskati Boga in narediti ponižno prošnjo Vsemogočnemu,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
če bi bil ti čist in pravičen, bi se on sedaj zaradi tebe zagotovo prebudil in prebivališče tvoje pravičnosti naredil uspešno.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Čeprav je bil tvoj začetek majhen, bi vendar tvoj zadnji konec silno narasel.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Kajti poizvedi, prosim te, o prejšnjem času in se pripravi, da preiskuješ o njihovih očetih
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
(kajti mi smo samo od včeraj in ne vemo nič, ker so naši dnevi na zemlji senca).
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Mar te ne bodo poučili in ti povedali in izustili besed iz svojega srca?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Mar lahko loček zraste brez blata? Mar lahko perunika raste brez vode?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Medtem ko je še v svojem zelenju in ni odtrgana, ovene pred katerimkoli drugim zeliščem.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Takšne so steze vseh, ki pozabljajo Boga in upanje hinavca bo propadlo,
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
katerega upanje bo odrezano, katerega trdno upanje bo pajkova mreža.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Naslonil se bo na svojo hišo, toda ta ne bo obstala; trdno jo bo držal, toda ta ne bo zdržala.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Zelen je pred soncem in njegova veja poganja v njegovem vrtu.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
Njegove korenine so ovite okoli kupa in strmi na kraj kamnov.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Če ga uniči iz svojega kraja, potem ga bo ta zatajil, rekoč: ›Nisem te videl.‹
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Glej, to je radost njegove poti in iz zemlje bodo pognali drugi.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Glej, Bog ne bo zavrnil popolnega moža niti ne bo pomagal hudodelcem,
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
dokler tvojih ust ne napolni s smehom in tvojih ustnic z radostjo.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Tisti, ki te sovražijo, bodo oblečeni s sramoto in bivališče zlobnega bo prišlo v nič.«

< Ayuba 8 >