< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Então Bildade, o suíta, respondeu, dizendo:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
Até quando falarás tais coisas, e as palavras de tua boca serão como um vento impetuoso?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Por acaso Deus perverteria o direito, ou o Todo-Poderoso perverteria a justiça?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Se teus filhos pecaram contra ele, ele também os entregou ao castigo por sua transgressão.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Se tu buscares a Deus com empenho, e pedires misericórdia ao Todo-Poderoso;
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
Se fores puro e correto, certamente logo ele se levantará em teu favor, e restaurará a morada de tua justiça.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Ainda que teu princípio seja pequeno, o teu fim será muito grandioso.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Pois pergunta agora à geração passada, e considera o que seus pais descobriram.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
Pois nós somos de ontem e nada sabemos, pois nossos dias sobre a terra são como a sombra.
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Por acaso eles não te ensinarão, e te dirão, e falarão palavras de seu coração?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Pode o papiro crescer sem lodo? Ou pode o junco ficar maior sem água?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Estando ele ainda verde, sem ter sido cortado, ainda assim se seca antes de toda erva.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Assim são os caminhos de todos os que esquecem de Deus; e a esperança do corrupto perecerá;
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Sua esperança será frustrada, e sua confiança será como a teia de aranha.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Ele se apoiará em sua casa, mas ela não ficará firme; ele se apegará a ela, mas ela não ficará de pé.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Ele está bem regado diante do sol, e seus ramos brotam por cima de sua horta;
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
Suas raízes se entrelaçam junto à fonte, olhando para o pedregal.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Se lhe arrancarem de seu lugar, este o negará, [dizendo]: Nunca te vi.
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Eis que este é o prazer de seu caminho; e do solo outros brotarão.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Eis que Deus não rejeita ao íntegro, nem segura pela mão aos malfeitores.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Ainda ele encherá tua boca de riso, e teus lábios de júbilo.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Os que te odeiam se vestirão de vergonha, e nunca mais haverá tenda de perversos.

< Ayuba 8 >