< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
آنگاه بلدد شوحی پاسخ داد:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
ای ایوب، تا به کی به این حرفها ادامه می‌دهی؟ حرفهای تو باد هواست!
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
آیا خدای قادر مطلق عدالت و انصاف را زیر پا می‌گذارد؟
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
فرزندانت به خدا گناه کردند و او به حق، ایشان را مجازات نمود.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
ولی اکنون تو به درگاه خدای قادر مطلق دعا کن.
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
اگر آدم پاک و خوبی باشی، او دعایت را می‌شنود و تو را اجابت می‌کند و خانهٔ تو را برکت می‌دهد.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
عاقبت تو آنچنان از خیر و برکت سرشار خواهد شد که زندگی گذشته‌ات در برابر آن ناچیز به نظر خواهد آمد.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
از سالخوردگان بپرس تا از تجربهٔ خود به تو بیاموزند.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
ما آنقدر زندگی نکرده‌ایم که همه چیز را بدانیم.
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
تو می‌توانی از حکمت گذشتگان درس عبرت بگیری و آنها به تو خواهند گفت که
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
آیا گیاه پاپیروس می‌تواند خارج از مرداب بروید؟ آیا علف مرداب بدون آب نمی‌میرد؟
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
آیا در حالی که هنوز سبز است و آماده بریدن نیست پژمرده نمی‌شود؟
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
همچنین است سرنوشت آنانی که خدا را فراموش می‌کنند. امید شخص بی‌خدا ناپایدار است.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
شخص بی‌خدا مانند کسی است که به تار عنکبوت اعتماد کند.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
اگر به آن تکیه نماید، می‌افتد و اگر از آن آویزان شود، آن تار او را نگه نمی‌دارد.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
او مانند گیاهی است که صبحگاهان تر و تازه می‌شود و شاخه‌هایش در باغ گسترده می‌گردند.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
در میان سنگها ریشه می‌دواند و خود را محکم نگه می‌دارد.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
ولی وقتی آن را از ریشه می‌کنند دیگر کسی آن را به یاد نمی‌آورد،
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
و گیاهان دیگری روییده جای آن را می‌گیرند. چنین است عاقبت شخص بی‌خدا.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
ولی بدان که خدا نیکان را ترک نمی‌گوید و بدکاران را کامیاب نمی‌گرداند.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
او بار دیگر دهانت را از خنده و فریادهای شادی پر خواهد کرد،
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
و دشمنانت را رسوا و خانهٔ شریران را خراب خواهد نمود.

< Ayuba 8 >