< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
پس بلدد شوحی در جواب گفت:۱
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
«تا به کی این چیزها را خواهی گفت و سخنان دهانت باد شدید خواهد بود؟۲
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
آیا خداوندداوری را منحرف سازد؟ یا قادر مطلق انصاف رامنحرف نماید؟۳
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
چون فرزندان تو به او گناه ورزیدند، ایشان را به‌دست عصیان ایشان تسلیم نمود.۴
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
اگر تو به جد و جهد خدا را طلب می‌کردی و نزد قادر مطلق تضرع می‌نمودی،۵
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
اگر پاک و راست می‌بودی، البته برای تو بیدارمی شد، و مسکن عدالت تو را برخوردارمی ساخت.۶
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
و اگر‌چه ابتدایت صغیر می‌بود، عاقبت تو بسیار رفیع می‌گردید.۷
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
زیرا که ازقرنهای پیشین سوال کن، و به آنچه پدران ایشان تفحص کردند توجه نما،۸
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
چونکه ما دیروزی هستیم و هیچ نمی دانیم، و روزهای ما سایه‌ای برروی زمین است.۹
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
آیا ایشان تو را تعلیم ندهند وبا تو سخن نرانند؟ و از دل خود کلمات بیرون نیارند؟۱۰
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
آیا نی، بی‌خلاب می‌روید، یا قصب، بی‌آب نمو می‌کند؟۱۱
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
هنگامی که هنوز سبزاست و بریده نشده، پیش از هر گیاه خشک می‌شود.۱۲
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
همچنین است راه جمیع فراموش کنندگان خدا. و امید ریاکار ضایع می شود،۱۳
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
که امید او منقطع می‌شود، واعتمادش خانه عنکبوت است.۱۴
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
بر خانه خودتکیه می‌کند و نمی ایستد، به آن متمسک می‌شودو لیکن قایم نمی ماند.۱۵
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
پیش روی آفتاب، تر وتازه می‌شود و شاخه هایش در باغش پهن می‌گردد.۱۶
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
ریشه هایش بر توده های سنگ درهم بافته می‌شود، و بر سنگلاخ نگاه می‌کند.۱۷
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
اگر ازجای خود کنده شود، او را انکار کرده، می‌گوید: تو را نمی بینم.۱۸
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
اینک خوشی طریقش همین است و دیگران از خاک خواهند رویید.۱۹
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
هماناخدا مرد کامل را حقیر نمی شمارد، و شریر رادستگیری نمی نماید،۲۰
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
تا دهان تو را از خنده پرکند، و لبهایت را از آواز شادمانی.۲۱
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
خصمان توبه خجالت ملبس خواهند شد، و خیمه شریران نابود خواهد گردید.»۲۲

< Ayuba 8 >