< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Respondens autem Baldad Suhites, dixit:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
[Usquequo loqueris talia, et spiritus multiplex sermones oris tui?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Numquid Deus supplantat judicium? aut Omnipotens subvertit quod justum est?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Etiam si filii tui peccaverunt ei, et dimisit eos in manu iniquitatis suæ:
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
tu tamen si diluculo consurrexeris ad Deum, et Omnipotentem fueris deprecatus;
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
si mundus et rectus incesseris: statim evigilabit ad te, et pacatum reddet habitaculum justitiæ tuæ,
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
in tantum ut si priora tua fuerint parva, et novissima tua multiplicentur nimis.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Interroga enim generationem pristinam, et diligenter investiga patrum memoriam
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
(hesterni quippe sumus, et ignoramus, quoniam sicut umbra dies nostri sunt super terram),
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
et ipsi docebunt te, loquentur tibi, et de corde suo proferent eloquia.
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Numquid vivere potest scirpus absque humore? aut crescere carectum sine aqua?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Cum adhuc sit in flore, nec carpatur manu, ante omnes herbas arescit.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Sic viæ omnium qui obliviscuntur Deum, et spes hypocritæ peribit.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Non ei placebit vecordia sua, et sicut tela aranearum fiducia ejus.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Innitetur super domum suam, et non stabit; fulciet eam, et non consurget.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Humectus videtur antequam veniat sol, et in ortu suo germen ejus egredietur.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
Super acervum petrarum radices ejus densabuntur, et inter lapides commorabitur.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Si absorbuerit eum de loco suo, negabit eum, et dicet: Non novi te.
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Hæc est enim lætitia viæ ejus, ut rursum de terra alii germinentur.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Deus non projiciet simplicem, nec porriget manum malignis,
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
donec impleatur risu os tuum, et labia tua jubilo.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Qui oderunt te induentur confusione, et tabernaculum impiorum non subsistet.]

< Ayuba 8 >