< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Allora Bildad di Suach rispose e disse:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
“Fino a quando terrai tu questi discorsi e saran le parole della tua bocca come un vento impetuoso?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Iddio perverte egli il giudizio? L’Onnipotente perverte egli la giustizia?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Se i tuoi figliuoli han peccato contro lui, egli li ha dati in balìa del loro misfatto;
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
ma tu, se ricorri a Dio e implori grazia dall’Onnipotente,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
se proprio sei puro e integro, certo egli sorgerà in tuo favore, e restaurerà la dimora della tua giustizia.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Così sarà stato piccolo il tuo principio, ma la tua fine sarà grande oltre modo.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Interroga le passate generazioni, rifletti sull’esperienza de’ padri;
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
giacché noi siam d’ieri e non sappiamo nulla; i nostri giorni sulla terra non son che un’ombra;
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
ma quelli certo t’insegneranno, ti parleranno, e dal loro cuore trarranno discorsi.
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Può il papiro crescere ove non c’è limo? Il giunco viene egli su senz’acqua?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Mentre son verdi ancora, e senza che li si tagli, prima di tutte l’erbe, seccano.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Tale la sorte di tutti quei che dimenticano Dio, e la speranza dell’empio perirà.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
La sua baldanza è troncata, la sua fiducia e come una tela di ragno.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Egli s’appoggia alla sua casa, ma essa non regge; vi s’aggrappa, ma quella non sta salda.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Egli verdeggia al sole, e i suoi rami si protendono sul suo giardino;
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
le sue radici s’intrecciano sul mucchio delle macerie, penetra fra le pietre della casa.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Ma divelto che sia dal suo luogo, questo lo rinnega e gli dice: “Non ti ho mai veduto!”
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Ecco il gaudio che gli procura la sua condotta! E dalla polvere altri dopo lui germoglieranno.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
No, Iddio non rigetta l’uomo integro, ne porge aiuto a quelli che fanno il male.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Egli renderà ancora il sorriso alla tua bocca, e sulle tue labbra metterà canti d’esultanza.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Quelli che t’odiano saran coperti di vergogna, e la tenda degli empi sparirà”.

< Ayuba 8 >