< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Alors Bildad Suhite prit la parole, et dit:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
Jusqu'à quand parleras-tu ainsi, et les paroles de ta bouche seront-elles comme un vent impétueux?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Le [Dieu] Fort renverserait-il le droit, et le Tout-puissant renverserait-il la justice?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Si tes enfants ont péché contre lui, il les a aussi livrés en la main de leur crime.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
[Mais] si tu recherches le [Dieu] Fort de bon matin, et que tu demandes grâce au Tout-puissant;
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
Si tu es pur et droit, certainement il se réveillera pour toi, et fera prospérer la demeure de ta justice.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Et ton commencement aura été petit, mais ta dernière condition sera beaucoup accrue.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Car, je te prie, enquiers-toi des générations précédentes, et applique-toi à t'informer soigneusement de leurs pères.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
Car nous ne sommes que du jour d'hier, et nous ne savons rien; parce que nos jours sont sur la terre comme une ombre.
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Ceux-là ne t'enseigneront-ils pas, ne te parleront-ils pas, et ne tireront-ils pas des discours de leur cœur?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Le jonc montera-t-il sans qu'il y ait du limon? l'herbe des marais croîtra-t-elle sans eau?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Ne se flétrira-t-elle pas même avant toute herbe, bien qu'elle soit encore en sa verdure, et qu'on ne la cueille point?
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Il en sera ainsi des voies de tous ceux qui oublient le [Dieu] Fort; et l'espérance de l'hypocrite périra.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Son espérance sera frustrée, et sa confiance sera [comme] une toile d'araignée.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Il s'appuiera sur sa maison, et elle n'aura point de fermeté; il la saisira de la main, et elle ne demeurera point debout.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Mais [l'homme intègre] est plein de vigueur étant exposé au soleil, et ses jets poussent par dessus son jardin.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
Ses racines s'entrelacent près de la fontaine, et il embrasse le bâtiment de pierre.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Fera-t-on qu'il ne soit plus en sa place, et que [le lieu où il était] le renonce, [en lui disant]: Je ne t'ai point vu?
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Voilà, quelle est la joie qu'il a de sa voie, même il en germera d'autres de la poussière.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Voilà, le [Dieu] Fort ne rejette point l'homme intègre; mais il ne soutient point la main des méchants.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
De sorte qu'il remplira ta bouche de ris, et tes lèvres de chants d'allégresse.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Ceux qui te haïssent seront revêtus de honte, et le tabernacle des méchants ne sera plus.

< Ayuba 8 >