< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Alors Baldad de Suhé prit la parole et dit:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
Jusques à quand tiendras-tu ces discours, et tes paroles seront-elles comme un souffle de tempête?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Est-ce que Dieu fait fléchir le droit, ou bien le Tout-Puissant renverse-t-il la justice?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Si tes fils ont péché contre lui, il les a livrés aux mains de leur iniquité.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Pour toi, si tu as recours à Dieu, si tu implores le Tout-Puissant,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
si tu es droit et pur, alors il veillera sur toi, il rendra le bonheur à la demeure de ta justice;
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
ton premier état semblera peu de chose, tant le second sera florissant.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Interroge les générations passées, sois attentif à l’expérience des pères: —
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
car nous sommes d’hier, et nous ne savons rien, nos jours sur la terre passent comme l’ombre; —
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
ne vont-ils pas t’enseigner, te parler, et de leur cœur tirer des sentences:
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
« Le papyrus croît-il en dehors des marais? Le jonc s’élève-t-il sans eau?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Encore tendre, sans qu’on le coupe, il sèche avant toute herbe.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Telles sont les voies de tous ceux qui oublient Dieu; l’espérance de l’impie périra.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Sa confiance sera brisée; son assurance ressemble à la toile de l’araignée.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Il s’appuie sur sa maison, et elle ne tient pas; il s’y attache, et elle ne reste pas debout.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Il est plein de vigueur, au soleil, ses rameaux s’étendent sur son jardin,
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
ses racines s’entrelacent parmi les pierres, il plonge jusqu’aux profondeurs du roc.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Si Dieu l’arrache de sa place, sa place le renie: Je ne t’ai jamais vu.
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
C’est là que sa joie se termine, et du même sol d’autres s’élèveront après lui. »
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Non, Dieu ne rejette pas l’innocent, il ne prend pas la main des malfaiteurs.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Il remplira ta bouche d’éclats de rire, et mettra sur tes lèvres des chants d’allégresse.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Tes ennemis seront couverts de honte, et la tente des méchants disparaîtra.

< Ayuba 8 >