< Ayuba 8 >
1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
And Bildad the Shuhite answers and says:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
“Until when do you speak these things? And a strong wind—sayings of your mouth?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Does God pervert judgment? And does the Mighty One pervert justice?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
If your sons have sinned before Him, And He sends them away, By the hand of their transgression,
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
If you seek for God early, And make supplication to the Mighty,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
If you [are] pure and upright, Surely now He wakes for you, And has completed The habitation of your righteousness.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
And your beginning has been small, And your latter end is very great.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
For inquire, please, of a former generation, And prepare for a search of their fathers,
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
For we [are] of yesterday, and we do not know, For our days [are] a shadow on earth.
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Do they not show you—speak to you, And from their heart bring forth words?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Does a rush rise without a marsh? A reed increase without water?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
While it [is] in its budding—uncropped, Even before any herb it withers.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
So [are] the paths of all forgetting God, And the hope of the profane perishes,
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Whose confidence is loathsome, And the house of a spider his trust.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
He leans on his house—and it does not stand, He takes hold on it—and it does not abide.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
He [is] green before the sun, And over his garden his branch goes out.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
His roots are wrapped by a heap, He looks for a house of stones.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
If [one] destroys him from his place, Then it has feigned concerning him, I have not seen you!
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Behold, this [is] the joy of His way, And from the dust others spring up.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Behold, God does not reject the perfect, Nor takes hold on the hand of evildoers.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
While He fills your mouth with laughter, And your lips with shouting,
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Those hating you put on shame, And the tent of the wicked is not!”