< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then answered Bildad the Shuhite, and saide,
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
Howe long wilt thou talke of these things? and howe long shall the wordes of thy mouth be as a mightie winde?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Doeth God peruert iudgement? or doeth the Almightie subuert iustice?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
If thy sonnes haue sinned against him, and he hath sent them into the place of their iniquitie,
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Yet if thou wilt early seeke vnto God, and pray to the Almightie,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
If thou be pure and vpright, then surely hee will awake vp vnto thee, and he wil make the habitation of thy righteousnesse prosperous.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
And though thy beginning be small, yet thy latter ende shall greatly encrease.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Inquire therefore, I pray thee, of the former age, and prepare thy selfe to search of their fathers.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
(For we are but of yesterday, and are ignorant: for our dayes vpon earth are but a shadowe)
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Shall not they teach thee and tell thee, and vtter the wordes of their heart?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Can a rush grow without myre? or can ye grasse growe without water?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Though it were in greene and not cutte downe, yet shall it wither before any other herbe.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
So are the paths of al that forget God, and the hypocrites hope shall perish.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
His confidence also shalbe cut off, and his trust shalbe as the house of a spyder.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
He shall leane vpon his house, but it shall not stand: he shall holde him fast by it, yet shall it not endure.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
The tree is greene before the sunne, and the branches spread ouer the garden thereof.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
The rootes thereof are wrapped about the fountaine, and are folden about ye house of stones.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
If any plucke it from his place, and it denie, saying, I haue not seene thee,
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Beholde, it will reioyce by this meanes, that it may growe in another molde.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Behold, God will not cast away an vpright man, neither will he take the wicked by the hand,
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Till he haue filled thy mouth with laughter, and thy lippes with ioy.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
They that hate thee, shall be clothed with shame, and the dwelling of the wicked shall not remaine.

< Ayuba 8 >