< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Tedy odpovídaje Bildad Suchský, řekl:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
Dokudž mluviti budeš takové věci, a slova úst tvých budou jako vítr násilný?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Což by Bůh silný neprávě soudil, a Všemohoucí což by převracel spravedlnost?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Synové zajisté tvoji že zhřešili proti němu, proto pustil je po nepravosti jejich.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Kdybys ty opravdově hledal Boha silného, a Všemohoucímu se modlil,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
A byl čistý a upřímý: jistě žeť by se hned probudil k tobě, a napravil by příbytek spravedlnosti tvé.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
A byly by první věci tvé špatné, poslední pak rozmnožily by se náramně.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Nebo vzeptej se, prosím, věku starého, a nastroj se k zpytování otců jejich.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
(Myť zajisté včerejší jsme, aniž jsme čeho povědomi; k tomu dnové naši jsou jako stín na zemi.)
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Zdaliž tě oni nenaučí, a nepovědí tobě, a z srdce svého nevynesou-liž slov?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Zdali roste třtí bez bahna? Roste-liž rákosí bez vody?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Nýbrž ještě za zelena, dříve než vytrháno bývá, ano prvé než jaká jiná tráva, usychá.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Tak stezky všech zapomínajících se na Boha silného, tak, pravím, naděje pokrytce zahyne.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Klesne naděje jeho, a doufání jeho jako dům pavouka.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Spolehne-li na dům svůj, neostojí; chytí-li se ho, nezdrží.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Vláhu má před sluncem, tak že z zahrady jeho výstřelkové jeho vynikají.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
Při vrchovišti kořenové jeho hustě rostou, i na místech skalnatých rozkládá se.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
A však bývá-li zachvácen z místa svého, až by se ho i odečtlo, řka: Nevidělo jsem tě:
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Tožť ta radost života jeho, a z země jiný vykvetá.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Aj, Bůh silný nepohrdá upřímým, ale nešlechetným ruky nepodává:
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Až i naplní smíchem ústa tvá, a rty tvé plésáním,
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Když nenávidící tebe v hanbu oblečeni budou, a stánku lidí bezbožných nikdež nebude.

< Ayuba 8 >