< Ayuba 7 >
1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
Не определено ли человеку время на земле, и дни его не то же ли, что дни наемника?
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
Как раб жаждет тени, и как наемник ждет окончания работы своей,
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
так я получил в удел месяцы суетные, и ночи горестные отчислены мне.
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
Когда ложусь, то говорю: “когда-то встану?”, а вечер длится, и я ворочаюсь досыта до самого рассвета.
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
Тело мое одето червями и пыльными струпами; кожа моя лопается и гноится.
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
Дни мои бегут скорее челнока и кончаются без надежды.
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
Вспомни, что жизнь моя дуновение, что око мое не возвратится видеть доброе.
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
Не увидит меня око видевшего меня; очи Твои на меня, - и нет меня.
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
Редеет облако и уходит; так нисшедший в преисподнюю не выйдет, (Sheol )
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
не возвратится более в дом свой, и место его не будет уже знать его.
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
Не буду же я удерживать уст моих; буду говорить в стеснении духа моего; буду жаловаться в горести души моей.
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
Разве я море или морское чудовище, что Ты поставил надо мною стражу?
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
Когда подумаю: утешит меня постель моя, унесет горесть мою ложе мое,
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
ты страшишь меня снами и видениями пугаешь меня;
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
и душа моя желает лучше прекращения дыхания, лучше смерти, нежели сбережения костей моих.
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
Опротивела мне жизнь. Не вечно жить мне. Отступи от меня, ибо дни мои суета.
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
Что такое человек, что Ты столько ценишь его и обращаешь на него внимание Твое,
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
посещаешь его каждое утро, каждое мгновение испытываешь его?
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
Доколе же Ты не оставишь, доколе не отойдешь от меня, доколе не дашь мне проглотить слюну мою?
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
Если я согрешил, то что я сделаю Тебе, страж человеков! Зачем Ты поставил меня противником Себе, так что я стал самому себе в тягость?
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
И зачем бы не простить мне греха и не снять с меня беззакония моего? ибо, вот, я лягу в прахе; завтра поищешь меня, и меня нет.