< Ayuba 7 >

1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
«آیا برای انسان بر زمین مجاهده‌ای نیست؟ و روزهای وی مثل روزهای مزدور نی؟۱
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
مثل غلام که برای سایه اشتیاق دارد، و مزدوری که منتظر مزد خویش است،۲
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
همچنین ماههای بطالت نصیب من شده است، و شبهای مشقت برای من معین گشته.۳
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
چون می‌خوابم می‌گویم: کی برخیزم؟ و شب بگذرد و تا سپیده صبح ازپهلو به پهلو گردیدن خسته می‌شوم.۴
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
جسدم ازکرمها و پاره های خاک ملبس است، و پوستم تراکیده و مقروح می‌شود.۵
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
روزهایم از ماکوی جولا تیزروتر است، و بدون امید تمام می‌شود.۶
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
به یاد آور که زندگی من باد است، و چشمانم دیگر نیکویی را نخواهد دید.۷
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
چشم کسی‌که مرامی بیند دیگر به من نخواهد نگریست، وچشمانت برای من نگاه خواهد کرد و نخواهم بود.۸
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
مثل ابر که پراکنده شده، نابود می‌شود. همچنین کسی‌که به گور فرو می‌رود، برنمی آید. (Sheol h7585)۹
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
به خانه خود دیگر نخواهد برگشت، و مکانش باز او را نخواهد شناخت.۱۰
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
پس من نیز دهان خود را نخواهم بست. از تنگی روح خود سخن می‌رانم، و از تلخی جانم شکایت خواهم کرد.۱۱
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
آیا من دریا هستم یا نهنگم که بر من کشیکچی قرار می‌دهی؟۱۲
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
چون گفتم که تخت خوابم مراتسلی خواهد داد و بسترم شکایت مرا رفع خواهد کرد،۱۳
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
آنگاه مرا به خوابها ترسان گردانیدی، و به رویاها مرا هراسان ساختی.۱۴
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
به حدی که جانم خفه شدن را اختیار کرد و مرگ رابیشتر از این استخوانهایم.۱۵
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
کاهیده می‌شوم ونمی خواهم تا به ابد زنده بمانم. مرا ترک کن زیراروزهایم نفسی است.۱۶
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
«انسان چیست که او را عزت بخشی، و دل خود را با او مشغول سازی؟۱۷
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
و هر بامداد از اوتفقد نمایی و هرلحظه او را بیازمایی؟۱۸
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
تا به کی چشم خود را از من برنمی گردانی؟ مرا واگذار تاآب دهان خود را فرو برم.۱۹
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
من گناه کردم، اما با تو‌ای پاسبان بنی آدم چه کنم؟ برای چه مرا به جهت خود هدف ساخته‌ای، به حدی که برای خود بار سنگین شده‌ام؟۲۰
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
و چرا گناهم رانمی آمرزی، و خطایم را دور نمی سازی؟ زیرا که الان در خاک خواهم خوابید، و مرا تفحص خواهی کرد و نخواهم بود.»۲۱

< Ayuba 7 >