< Ayuba 7 >

1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
“People need to work hard on this earth, like soldiers do; all during the time that we are alive, we work hard [RHQ], like laborers/servants do.
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
We are like [SIM] slaves who keep wanting to be in the cool shade, and we are like [SIM] workers who are waiting to be paid.
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
God has given me many months [in which I think that it is] useless [to remain alive]; he has allotted/given to me many nights during which I feel miserable.
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
When I lie down [at night] I say, ‘How long will it be until morning?’ But nights are long, and I (toss/turn over and over) [on my bed] until dawn.
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
My body is covered with maggots and scabs; pus oozes out of my open sores.
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
My days pass as quickly as a weaver’s (shuttle/stick that takes the thread back and forth), and they end without my confidently expecting [that things will be better the next day].
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
God, do not forget that my life is [as short as] a breath [MET]; I [think that] I [SYN] will never again be happy.
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
God, you [SYN] see me now, but [some day] you will not see me any more. You will search for me, but I will be gone [because I will be dead].
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
Like [SIM] clouds (disperse/break up) and then disappear, people [die and] descend to the place where dead people are, and they do not return; (Sheol h7585)
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
they never return to their houses, and people among whom they lived do not remember them any more.
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
So, I will not be silent; while I am suffering I will speak; I will complain [to God about what has happened to me] because I [SYN] am very angry.
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
[God, ] why do you watch closely what I am doing? [Do you think that] I am a [dangerous] sea monster?
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
When [I lie down at night, ] I think, ‘I will be comforted here on my bed; my pain will be less while I am sleeping.’
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
But then you give me dreams that cause me to be afraid; you give me visions that terrify me,
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
with the result that I would prefer to be strangled to death than to continue to [be alive] being only a bunch of bones.
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
I detest continuing to be alive; I do not want to live for many years [HYP]. Allow me to be alone, [because I will be alive] for only a very short remaining time [HYP].
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
“We human beings are not [very important]; so, why do you pay a lot of attention to us [DOU]?
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
You look at us every morning [to see what we are doing], and examine us every moment [to see if we are doing what is right].
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
(When will you stop looking at me and leave me alone [for a little time], long enough to swallow my spit?/Please stop looking at me and leave me alone [for a little time], long enough to swallow my spit.) [RHQ]
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
[Why do] you watch me constantly? If I sin, that certainly does not harm you! Why have you set me up like a target to shoot at? Do you consider me to be a heavy load that you are forced to carry?
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
[If I have sinned, ] are you not able to forgive me for my sins— the things that I have done that are wrong? Soon I will lie in my grave; you will search for me, but [you will not find me because] I will be [dead and] gone.”

< Ayuba 7 >