< Ayuba 7 >

1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
Is there not a war-service for man on the earth? Are not his days as the days of a hireling?
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
As a servant panteth for the shade, And as a hireling looketh for his wages,
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
So am I made to possess months of affliction, And wearisome nights are appointed for me.
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
If I lie down, I say, When shall I arise, and the night be gone? And I am full of restlessness until the dawning of the day.
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
My flesh is clothed with worms, and clods of dust; My skin is broken and become loathsome.
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
My days are swifter than a weaver's shuttle; They pass away without hope.
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
O remember that my life is a breath; That mine eye shall no more see good!
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
The eye of him that hath seen me shall see me no more; Thine eyes shall look for me, but I shall not be.
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
As the cloud dissolveth and wasteth away, So he that goeth down to the grave shall arise no more; (Sheol h7585)
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
No more shall he return to his house, And his dwelling-place shall know him no more.
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
Therefore I will not restrain my mouth; I will speak in the anguish of my spirit; I will complain in the bitterness of my soul.
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
Am I a sea, or a sea-monster, That thou settest a watch over me?
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
When I say, My bed shall relieve me, My couch shall ease my complaint,
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
Then thou scarest me with dreams, And terrifiest me with visions;
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
So that my soul chooseth strangling, Yea, death, rather than these my bones.
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
I am wasting away; I shall not live alway: Let me alone, for my days are a vapor!
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
What is man, that thou shouldst make great account him, And fix thy mind upon him?—
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
That thou shouldst visit him every morning, And prove him every moment?
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
How long ere thou wilt look away from me, And let me alone, till I have time to breathe?
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
If I have sinned, what have I done to thee, O thou watcher of men! Why hast thou set me up as thy mark, So that I have become a burden to myself?
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
And why dost thou not pardon my transgression, And take away mine iniquity? For soon shall I sleep in the dust; And, though thou seek me diligently, I shall not be.

< Ayuba 7 >