< Ayuba 7 >

1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
Is there not a limited time of service to a mortal upon the earth? Are not his days also like the days of a hired laborer?
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
As a servant eagerly longeth for the shadow, and as a hired laborer hopeth for his reward:
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
So was I compelled to possess months of vanity, and nights of trouble were counted out unto me.
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
When I He down, I say, When shall I arise, and the night be gone? and I am wearied with tossings about till the dawn of day.
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
My flesh is covered with worms and clods of dust: my skin is burst open, and become loathsome.
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
My days hasten away more swiftly than a weaver's shuttle, and they come to an end in the absence of hope.
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
Oh remember that nothing but a breath is my life; that my eye will not again see happiness;
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
The eye of him that seeth me now will not behold me again: [thou fixest] thy eyes upon me, and I am no more.
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
As the cloud vanisheth and passeth away: so will he that goeth down to the nether world not come up again. (Sheol h7585)
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
He will return no more to his house, and his place will not recognize him any more.
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
Therefore will I also not restrain my mouth: I will speak in the anguish of my spirit: I will complain in the bitterness of my soul.
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
Am I a sea, or a monster, that thou settest a watch over me?
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
For should I say, My bed shall comfort me, my couch shall help me bear my complaint:
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
Then wouldst thou frighten me with dreams, and with visions wouldst thou terrify me;
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
So that my soul would choose strangling, death rather than these limbs of mine.
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
I loathe it; I cannot live for ever: let me alone; for my days are but nought.
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
What is the mortal, that thou shouldst make him great? and that thou shouldst direct thy heart toward him?
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
And that thou shouldst visit him every morning, probe him every moment?
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
How long wilt thou not turn thy regard from me, nor let; me loose till I swallow down my spittle?
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
If I have sinned, what [injury] can I cause unto thee, O thou Guardian of men? why hast thou set me as an object for thee to strike at, so that I am become a burden to myself?
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
And why wilt thou not forgive my transgression, and let my iniquity pass away? for soon must I lie down in the dust; and thou wilt seek for me, but I shall be no more.

< Ayuba 7 >