< Ayuba 7 >
1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
Has not man his ordered time of trouble on the earth? and are not his days like the days of a servant working for payment?
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
As a servant desiring the shades of evening, and a workman looking for his payment:
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
So I have for my heritage months of pain to no purpose, and nights of weariness are given to me.
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
When I go to my bed, I say, When will it be time to get up? but the night is long, and I am turning from side to side till morning light.
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
My flesh is covered with worms and dust; my skin gets hard and then is cracked again.
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
My days go quicker than the cloth-worker's thread, and come to an end without hope.
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
O, keep in mind that my life is wind: my eye will never again see good.
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
The eye of him who sees me will see me no longer: your eyes will be looking for me, but I will be gone.
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
A cloud comes to an end and is gone; so he who goes down into the underworld comes not up again. (Sheol )
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
He will not come back to his house, and his place will have no more knowledge of him.
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
So I will not keep my mouth shut; I will let the words come from it in the pain of my spirit, my soul will make a bitter outcry.
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
Am I a sea, or a sea-beast, that you put a watch over me?
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
When I say, In my bed I will have comfort, there I will get rest from my disease;
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
Then you send dreams to me, and visions of fear;
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
So that a hard death seems better to my soul than my pains.
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
I have no desire for life, I would not be living for ever! Keep away from me, for my days are as a breath.
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
What is man, that you have made him great, and that your attention is fixed on him,
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
And that your hand is on him every morning, and that you are testing him every minute?
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
How long will it be before your eyes are turned away from me, so that I may have a minute's breathing-space?
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
If I have done wrong, what have I done to you, O keeper of men? why have you made me a mark for your blows, so that I am a weariness to myself?
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
And why do you not take away my sin, and let my wrongdoing be ended? for now I go down to the dust, and you will be searching for me with care, but I will be gone.