< Ayuba 7 >
1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
Har Mennesket paa Jord ej Krigerkaar? Som en Daglejers er hans Dage.
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
Som Trællen, der higer efter Skygge som Daglejeren, der venter paa Løn,
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
saa fik jeg Skuffelses Maaneder i Arv kvalfulde Nætter til Del.
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
Naar jeg lægger mig, siger jeg: »Hvornaar er det Dag, at jeg kan staa op?« og naar jeg staar op: »Hvornaar er det Kvæld?« Jeg mættes af Uro, til Dagen gryr.
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
Mit Legeme er klædt med Orme og Skorpe, min Hud skrumper ind og væsker.
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
Raskere end Skyttelen flyver mine Dage, de svinder bort uden Haab.
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
Kom i Hu, at mit Liv er et Pust, ej mer faar mit Øje Lykke at skue!
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
Vennens Øje skal ikke se mig, dit Øje søger mig — jeg er ikke mere.
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
Som Skyen svinder og trækker bort, bliver den, der synker i Døden, borte, (Sheol )
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
han vender ej atter hjem til sit Hus, hans Sted faar ham aldrig at se igen.
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
Saa vil jeg da ej lægge Baand paa min Mund, men tale i Aandens Kvide, sukke i bitter Sjælenød.
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
Er jeg et Hav, eller er jeg en Drage, siden du sætter Vagt ved mig?
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
Naar jeg tænker, mit Leje skal lindre mig, Sengen lette mit Suk,
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
da ængster du mig med Drømme, skræmmer mig op ved Syner,
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
saa min Sjæl vil hellere kvæles, hellere dø end lide.
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
Nu nok! Jeg lever ej evigt, slip mig, mit Liv er et Pust!
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
Hvad er et Menneske, at du regner ham og lægger Mærke til ham,
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
hjemsøger ham hver Morgen, ransager ham hvert Øjeblik?
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
Naar vender du dog dit Øje fra mig, slipper mig, til jeg har sunket mit Spyt?
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
Har jeg syndet, hvad skader det dig, du, som er Menneskets Vogter? Hvi gjorde du mig til Skive, hvorfor blev jeg dig til Byrde?
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
Hvorfor tilgiver du ikke min Synd og lader min Brøde uænset? Snart ligger jeg jo under Mulde, du søger mig — og jeg er ikke mere!