< Ayuba 6 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Entonces Job respondió:
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
¡Oh, si se pesara mi angustia, y se pusiera igualmente en balanza juntamente con mi ruina!
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
¡Pesarían ahora más que la arena del mar! Por eso mis palabras fueron precipitadas,
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
porque en mí están clavadas las flechas de ʼEL-Shadday. Mi espíritu sorbe su veneno, y terrores de ʼElohim me combaten.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
¿Rebuzca el asno montés junto a la hierba? ¿Muge el buey junto a su pasto?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
¿Se comerá lo insípido sin sal? ¿Hay sabor en la clara del huevo?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
Las cosas que mi alma rehusaba tocar son ahora mi alimento nauseabundo.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
¡Quién me diera obtener mi petición, y que ʼElohim me otorgue lo que tanto anhelo!
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
¡Que ʼElohim se digne aplastarme, que suelte su mano y acabe conmigo!
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
Eso sería mi consuelo, y aun en medio de mi dolor que no da tregua, saltaría de gozo, porque no negué las Palabras del Santo.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
¿Cuál es mi fuerza para seguir esperando? ¿Cuál es mi propósito para que tenga aún paciencia?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
¿Es mi fortaleza como la de las piedras, o mi cuerpo es de bronce?
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
¿Puedo sostenerme sobre nada? ¿No fue todo auxilio alejado de mí?
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
Para el hombre desconsolado debe haber bondad de su amigo, a fin de que no abandone el temor a ʼEL-Shadday.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
Mis hermanos me traicionaron como un torrente. Pasan como corrientes impetuosas
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
que van turbias a causa del deshielo, y la nieve que se deshace en ellas.
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
En el tiempo del calor se desvanecen. Al calentarse desaparecen, se extinguen de su lugar.
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
Se apartan de la senda de su rumbo, van menguando y se pierden.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
Las caravanas de Temán fijan su mirada en ellas, los viajeros de Sabá tienen su esperanza en ellas,
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
pero son avergonzados en su esperanza, pues llegan hasta ellas y quedan defraudados.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
En verdad ustedes son ahora como ellos. Ven un terror y temen.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
¿Yo les dije: Tráiganme algo? ¿O: Paguen de su hacienda por mí?
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
¿O: Líbrenme de la mano del enemigo? ¿O: Rescátenme del poder del opresor?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Instrúyeme y me callaré. Hazme entender en qué erré.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
¡Cuán dolorosas son las palabras honestas! ¿Pero qué prueba su reprensión?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
¿Piensan ustedes censurar palabras y los dichos de un desesperado que son como el viento?
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Ustedes aun echan suertes sobre los huérfanos y regatean con su amigo.
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Ahora pues, dígnense mirarme y opinen si miento delante de ustedes.
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Les ruego que desistan. Que no haya iniquidad. Sí, que mi justicia aún permanezca.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
¿Hay iniquidad en mi lengua? ¿Mi paladar no distingue lo destructivo?