< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
욥이 대답하여 가로되
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
나의 분한을 달아 보며 나의 모든 재앙을 저울에 둘 수 있으면
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
바다 모래보다도 무거울 것이라 그럼으로 하여 나의 말이 경솔 하였구나
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
전능자의 살이 내 몸에 박히매 나의 영이 그 독을 마셨나니 하나님의 두려움이 나를 엄습하여 치는구나
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
들 나귀가 풀이 있으면 어찌 울겠으며 소가 꼴이 있으면 어찌 울겠느냐
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
싱거운 것이 소금 없이 먹히겠느냐 닭의 알 흰자위가 맛이 있겠느냐
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
이런 것을 만지기도 내 마음이 싫어하나니 못된 식물 같이 여김 이니라
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
하나님이 나의 구하는 것을 얻게 하시며 나의 사모하는 것 주시기를 내가 원하나니
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
이는 곧 나를 멸하시기를 기뻐하사 그 손을 들어 나를 끊으실 것이라
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
그러할지라도 내가 오히려 위로를 받고 무정한 고통 가운데서도 기뻐할 것은 내가 거룩하신 이의 말씀을 거역지 아니하였음이니라
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
내가 무슨 기력이 있관대 기다리겠느냐 내 마지막이 어떠하겠관대 오히려 참겠느냐
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
나의 기력이 어찌 돌의 기력이겠느냐 나의 살이 어찌 놋쇠겠느냐
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
나의 도움이 내 속에 없지 아니하냐 나의 지혜가 내게서 쫓겨나지 아니하였느냐
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
피곤한 자 곧 전능자 경외하는 일을 폐한 자를 그 벗이 불쌍히 여길 것이어늘
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
나의 형제는 내게 성실치 아니함이 시냇물의 마름 같고 개울의 잦음 같구나
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
얼음이 녹으면 물이 검어지며 눈이 그 속에 감취었을지라도
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
따뜻하면 마르고 더우면 그 자리에서 아주 없어지나니
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
떼를 지은 객들이 시냇가로 다니다가 돌이켜 광야로 가서 죽고
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
데마의 떼들이 그것을 바라보고 스바의 행인들도 그것을 사모하다가
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
거기 와서는 바라던 것을 부끄리고 낙심하느니라
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
너희도 허망한 자라 너희가 두려운 일을 본즉 겁내는구나
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
내가 언제 너희에게 나를 공급하라 하더냐 언제 나를 위하여 너희 재물로 예물을 달라더냐
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
내가 언제 말하기를 대적의 손에서 나를 구원하라 하더냐 포악한자의 손에서 나를 구속하라 하더냐
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
내게 가르쳐서 나의 허물된 것을 깨닫게 하라 내가 잠잠하리라
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
옳은 말은 어찌 그리 유력한지, 그렇지만 너희의 책망은 무엇을 책망함이뇨
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
너희가 말을 책망하려느냐 소망이 끊어진 자의 말은 바람 같으니라
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
너희는 고아를 제비 뽑으며 너희 벗을 매매할 자로구나
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
이제 너희가 나를 향하여 보기를 원하노라 내가 너희를 대면하여 결코 거짓말하지 아니하리라
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
너희는 돌이켜 불의한 것이 없게 하기를 원하노라 너희는 돌이키라 내 일이 의로우니라
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
내 혀에 어찌 불의한 것이 있으랴 내 미각이 어찌 궤휼을 분변치못하랴

< Ayuba 6 >