< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Allora Giobbe rispose e disse:
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
“Ah, se il mio travaglio si pesasse, se le mie calamità si mettessero tutte insieme sulla bilancia!
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
Sarebbero trovati più pesanti che la sabbia del mare. Ecco perché le mie parole sono temerarie.
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
Ché le saette dell’Onnipotente mi trafiggono, lo spirito mio ne sugge il veleno; i terrori di Dio si schierano in battaglia contro me.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
L’asino salvatico raglia forse quand’ha l’erba davanti? mugghia forse il bue davanti alla pastura?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
Si può egli mangiar ciò ch’è scipito e senza sale? c’è qualche gusto in un chiaro d’uovo?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
L’anima mia rifiuta di toccare una simil cosa, essa è per me come un cibo ripugnante.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Oh, m’avvenisse pur quello che chiedo, e mi desse Iddio quello che spero!
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
Volesse pure Iddio schiacciarmi, stender la mano e tagliare il filo de’ miei giorni!
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
Sarebbe questo un conforto per me, esulterei nei dolori ch’egli non mi risparmia; giacché non ho rinnegato le parole del Santo.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
Che è mai la mia forza perch’io speri ancora? Che fine m’aspetta perch’io sia paziente?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
La mia forza è essa forza di pietra? e la mia carne, carne di rame?
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
Non son io ridotto senza energia, e non m’è forse tolta ogni speranza di guarire?
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
Pietà deve l’amico a colui che soccombe, quand’anche abbandoni il timor dell’Onnipotente.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
Ma i fratelli miei si son mostrati infidi come un torrente, come l’acqua di torrenti che passano.
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
Il ghiaccio li rende torbidi, e la neve vi si scioglie;
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
ma passato il tempo delle piene, svaniscono; quando sentono il caldo, scompariscono dal loro luogo.
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
Le carovane che si dirigon là mutano strada, s’inoltran nel deserto, e vi periscono.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
Le carovane di Tema li cercavan collo sguardo, i viandanti di Sceba ci contavan su,
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
ma furon delusi nella loro fiducia; giunti sul luogo, rimasero confusi.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
Tali siete divenuti voi per me: vedete uno che fa orrore, e vi prende la paura.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
V’ho forse detto: “Datemi qualcosa” o “co’ vostri beni fate un donativo a favor mio”,
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
o “liberatemi dalla stretta del nemico, o “scampatemi di man dei prepotenti”?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Ammaestratemi, e mi starò in silenzio; fatemi capire in che cosa ho errato.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
Quanto sono efficaci le parole rette! Ma la vostra riprensione che vale?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
Volete dunque biasimar delle parole? Ma le parole d’un disperato se le porta il vento!
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Voi sareste capaci di trar la sorte sull’orfano, e di contrattare il vostro amico!
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Ma pure vi piaccia di rivolgervi a guardarmi, e vedete s’io vi menta in faccia.
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Mutate consiglio! Non vi sia in voi iniquità! Mutate consiglio, la mia giustizia sussiste.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
V’è qualche iniquità sulla mia lingua? Il mio palato non distingue più quel ch’è male?

< Ayuba 6 >