< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
ויען איוב ויאמר
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
לו--שקול ישקל כעשי והיתי (והותי) במאזנים ישאו-יחד
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
כי-עתה--מחול ימים יכבד על-כן דברי לעו
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
כי חצי שדי עמדי--אשר חמתם שתה רוחי בעותי אלוה יערכוני
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
הינהק-פרא עלי-דשא אם יגעה-שור על-בלילו
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
היאכל תפל מבלי-מלח אם-יש-טעם בריר חלמות
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
מאנה לנגוע נפשי המה כדוי לחמי
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
מי-יתן תבוא שאלתי ותקותי יתן אלוה
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
ויאל אלוה וידכאני יתר ידו ויבצעני
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
ותהי-עוד נחמתי-- ואסלדה בחילה לא יחמול כי-לא כחדתי אמרי קדוש
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
מה-כחי כי-איחל ומה-קצי כי-אאריך נפשי
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
אם-כח אבנים כחי אם-בשרי נחוש
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
האם אין עזרתי בי ותשיה נדחה ממני
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
למס מרעהו חסד ויראת שדי יעזוב
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
אחי בגדו כמו-נחל כאפיק נחלים יעברו
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
הקדרים מני-קרח עלימו יתעלם-שלג
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
בעת יזרבו נצמתו בחמו נדעכו ממקומם
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
ילפתו ארחות דרכם יעלו בתהו ויאבדו
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
הביטו ארחות תמא הליכת שבא קוו-למו
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
בשו כי-בטח באו עדיה ויחפרו
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
כי-עתה הייתם לא תראו חתת ותיראו
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
הכי-אמרתי הבו לי ומכחכם שחדו בעדי
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
ומלטוני מיד-צר ומיד עריצים תפדוני
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
הורוני ואני אחריש ומה-שגיתי הבינו לי
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
מה-נמרצו אמרי-ישר ומה-יוכיח הוכח מכם
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
הלהוכח מלים תחשבו ולרוח אמרי נואש
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
אף-על-יתום תפילו ותכרו על-ריעכם
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
ועתה הואילו פנו-בי ועל-פניכם אם-אכזב
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
שובו-נא אל-תהי עולה ושבי (ושבו) עוד צדקי-בה
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
היש-בלשוני עולה אם-חכי לא-יבין הוות

< Ayuba 6 >