< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Hiob antwortete und sprach:
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
O daß man meinen Unmut wöge und mein Leid dagegen auf die Wage legte!
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
Denn nun ist's schwerer, als der Sand am Meer - drum gehen irre meine Worte!
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
Denn des Allmächtigen Pfeile stecken in mir: mein Geist saugt ihr Gift ein, die Schrecknisse Gottes verstören mich!
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
Schreit etwa der Wildesel auf grüner Weide, oder brüllt der Stier bei seinem Mengfutter?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
Kann man Fades ungesalzen genießen, oder hat das Eiweiß Wohlgeschmack?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
Mich widert's an, es anzurühren; es ekelt mich vor der Unreinigkeit meiner Speise.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
O daß doch mein Wunsch sich erfüllte, und Gott mein Verlangen gewährte!
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
Gefiele es Gott, mich zu zermalmen, seine Hand zu entfesseln und meinen Lebensfaden abzuschneiden!
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
So wäre doch das noch mein Trost und aufhüpfen wollte ich im schonungslosen Schmerz -, daß ich des Heiligen Worte nie verleugnet habe.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
Was ist denn meine Kraft, daß ich noch harren, und was mein Ende, daß ich mich gedulden sollte?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
Ist meine Kraft etwa Felsenkraft, oder ist mein Leib aus Erz?
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
Bin ich nicht der Hilfe bar, und ist nicht aller Halt von mir genommen?
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
Dem Verzagenden gebührt das Mitleid seines Nächsten, selbst wenn er von der Furcht vor dem Allmächtigen läßt.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
Meine Freunde haben sich treulos erzeigt wie ein Bach, wie die Rinnsale, die überschwellen,
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
die trübe sind von Eis, in die herab der Schnee sich birgt.
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
Wenn sie durchglüht werden, schwinden sie dahin: wenn's heiß wird, sind sie weggelöscht von ihrem Ort.
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
Karawanen biegen ab von ihrer Straße, ziehen hinauf in die Öde und kommen um.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
Die Karawanen Themas schauten aus, die Reisezüge Sabas warteten auf sie:
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
Sie wurden zu Schanden mit ihrem Vertrauen, kamen hin und wurden enttäuscht.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
So seid ihr nun für mich geworden: ihr schautet Schrecknis, - da scheutet ihr euch!
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
Habe ich etwa gesagt: “Schafft mir her und von eurer Habe spendet für mich;
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
errettet mich aus der Gewalt des Bedrängers und aus der Gewalt der Tyrannen kauft mich los”?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Belehrt mich, so will ich schweigen, und worin ich geirrt habe, thut mir kund.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
Wie eindringlich sind der Wahrheit Worte! aber was beweist denn euer Verweis?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
Gedenkt ihr, Worte zu rügen? Die Reden des Verzweifelten verhallen im Wind!
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Selbst über meine Waise würdet ihr losen und euren eignen Freund verhandeln.
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Und nun - wollet doch mich anblicken, ich werde euch doch wahrlich nicht ins Angesicht lügen!
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
O kehret um, laßt Unrecht nicht geschehen, ja, kehret um, noch hab' ich Recht hierin.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
Wohnt denn auf meiner Zunge Frevel, oder unterscheidet mein Gaumen nicht die Unglücksschläge?

< Ayuba 6 >