< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Et Job répondit et dit:
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
Oh! si mon chagrin était bien pesé, et si on mettait toute ma calamité dans la balance!
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
Car maintenant elle pèserait plus que le sable des mers; c’est pourquoi mes paroles sont outrées;
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
Car les flèches du Tout-puissant sont en moi, leur venin boit mon esprit; les frayeurs de Dieu se rangent en bataille contre moi.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
L’âne sauvage brait-il auprès de l’herbe? Le bœuf mugit-il auprès de son fourrage?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
Ce qui est insipide, le mange-t-on sans sel? Y a-t-il de la saveur dans le blanc d’un œuf?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
Ce que mon âme refusait de toucher est comme ma dégoûtante nourriture.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Oh! si ma demande s’accomplissait, et si Dieu m’accordait mon désir,
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
S’il plaisait à Dieu de m’écraser, de lâcher sa main et de me retrancher!
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
Alors il y aurait encore pour moi une consolation, et, dans la douleur qui ne m’épargne pas, je me réjouirais de ce que je n’ai pas renié les paroles du Saint.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
Quelle est ma force pour que j’attende, et quelle est ma fin pour que je patiente?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
Ma force est-elle la force des pierres? Ma chair est-elle d’airain?
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
N’est-ce pas qu’il n’y a point de secours en moi, et que toute capacité est chassée loin de moi?
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
À celui qui est défaillant est due la miséricorde de la part de son ami, sinon il abandonnera la crainte du Tout-puissant.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
Mes frères m’ont trahi comme un torrent, comme le lit des torrents qui passent,
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
Qui sont troubles à cause des glaces, dans lesquels la neige se cache;
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
Au temps où ils se resserrent ils tarissent, quand la chaleur les frappe ils disparaissent de leur lieu:
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
Ils serpentent dans les sentiers de leur cours, ils s’en vont dans le désert, et périssent.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
Les caravanes de Théma les cherchaient du regard, les voyageurs de Sheba s’attendaient à eux;
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
Ils ont été honteux de leur confiance; ils sont venus là, et ont été confondus.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
De même maintenant vous n’êtes rien; vous avez vu un objet de terreur, et vous vous êtes effrayés.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
Ai-je dit: Donnez-moi, et de votre richesse faites-moi des présents,
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
Et délivrez-moi de la main de l’oppresseur, et rachetez-moi de la main des terribles?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Enseignez-moi, et je me tairai; et faites-moi comprendre en quoi je me trompe.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
Combien sont puissantes les paroles justes! Mais la censure de votre part que reprend-elle?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
Songez-vous à censurer des discours? Mais les paroles d’un désespéré ne sont faites que pour le vent.
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Certes, vous tombez sur l’orphelin, et vous creusez [une fosse] pour votre ami.
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Et maintenant, si vous voulez, regardez-moi; vous mentirais-je donc en face?
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Revenez, je vous prie; qu’il n’y ait pas d’injustice; oui, revenez encore: ma justice sera là.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
Y a-t-il de l’iniquité en ma langue? Mon palais ne discernerait-il pas la méchanceté?

< Ayuba 6 >