< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
And he answered Job and he said.
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
Certainly [if] it will be weighed grief my (and destruction my *Q(K)*) in [the] balances people will raise together.
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
For now more than [the] sand of [the] seas it will be heavy there-fore words my they have been rash.
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
For [the] arrows of [the] Almighty [are] with me which poison their [is] drinking spirit my [the] terrors of God they are arranged against me.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
¿ Does it bray a wild donkey on grass or? does it low an ox on fodder its.
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
¿ Is it eaten tasteless [food] because not salt or? [is] there taste in [the] slime of purslane.
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
It refuses to touch [them] self my they [are] like [the] illness of food my.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Who? will he give it will come petition my and hope my he will give God.
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
And may he be willing God and may he crush me may he loosen hand his and may he cut off me.
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
And may it be still - comfort my and may I jump in anguish [which] not it relents that not I have hidden [the] words of [the] holy [one].
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
What? [is] strength my that I will wait and what? [is] end my that I will prolong life my.
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
[the] strength of Stones [is] strength my or? [is] flesh my bronze.
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
¿ If not [is] help my in myself and sound wisdom it has been banished from me.
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
[belongs] to Despairing [person] from friend his loyalty and [the] fear of [the] Almighty he will forsake.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
Brothers my they have acted treacherously like a wadi like a stream-bed of wadis [which] they pass away.
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
That are dark from ice over them it hides itself snow.
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
At [the] time [when] they flow they are silenced in heat its they are dried up from place their.
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
They twist [the] paths of way their they go up in the wasteland so they may perish.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
They look [the] caravans of Tema [the] travelers of Sheba they look eagerly for them.
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
They are disappointed for he had been confident they come to it and they were disappointed.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
For now you have become (it *Q(K)*) you have seen a terror and you were afraid.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
¿ For have I said give for me and from wealth your give a reward for me.
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
And rescue me from [the] hand of an opponent and from [the] hand of ruthless [people] you will ransom me.
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Teach me and I I will keep silent and what? have I erred explain to me.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
How! they are painful words of uprightness and what? does it prove completely from you.
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
¿ To reprove words do you plan and to wind [the] words of [one who] despairs.
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Even on a fatherless one you will make fall and you may bargain on friend your.
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
And therefore be willing turn on me and on faces your if I will lie.
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Turn back please may not it be injustice (and turn back *Q(K)*) still righteousness my [is] in it.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
¿ [is] there On tongue my injustice or? palate my not does it discern destruction.

< Ayuba 6 >