< Ayuba 6 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Bvt Iob answered, and said,
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
Oh that my griefe were well weighed, and my miseries were layed together in the balance.
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
For it woulde be nowe heauier then the sande of the sea: therefore my wordes are swallowed vp.
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
For the arrowes of the Almightie are in me, the venime whereof doeth drinke vp my spirit, and the terrours of God fight against me.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
Doeth the wilde asse bray when he hath grasse? or loweth the oxe when he hath fodder?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
That which is vnsauerie, shall it be eaten without salt? or is there any taste in the white of an egge?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
Such things as my soule refused to touch, as were sorowes, are my meate.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Oh that I might haue my desire, and that God would grant me the thing that I long for!
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
That is, that God would destroy me: that he would let his hand go, and cut me off.
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
Then should I yet haue comfort, (though I burne with sorowe, let him not spare) because I haue not denyed the wordes of the Holy one.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
What power haue I that I should endure? or what is mine end, if I should prolong my life?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
Is my strength the strength of stones? or is my flesh of brasse?
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
Is it not so, that there is in me no helpe? and that strength is taken from me?
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
He that is in miserie, ought to be comforted of his neighbour: but men haue forsaken the feare of the Almightie.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
My brethre haue deceiued me as a brook, and as the rising of the riuers they passe away.
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
Which are blackish with yee, and wherein the snowe is hid.
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
But in time they are dryed vp with heate and are consumed: and when it is hote they faile out of their places,
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
Or they depart from their way and course, yea, they vanish and perish.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
They that go to Tema, considered them, and they that goe to Sheba, waited for them.
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
But they were confounded: when they hoped, they came thither and were ashamed.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
Surely nowe are ye like vnto it: ye haue seene my fearefull plague, and are afraide.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
Was it because I said, Bring vnto me? or giue a rewarde to me of your substance?
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
And deliuer me from the enemies hande, or ransome me out of the hand of tyrants?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Teach me, and I wil hold my tongue: and cause me to vnderstande, wherein I haue erred.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
Howe stedfast are the wordes of righteousnes? and what can any of you iustly reproue?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
Doe ye imagine to reproue wordes, that the talke of the afflicted should be as the winde?
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Ye make your wrath to fall vpon the fatherlesse, and dig a pit for your friende.
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Nowe therefore be content to looke vpon me: for I will not lie before your face.
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Turne, I pray you, let there be none iniquitie: returne, I say, and ye shall see yet my righteousnesse in that behalfe.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
Is there iniquitie in my tongue? doeth not my mouth feele sorowes?