< Ayuba 6 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Then Job responded:
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
“If my grief could be weighed and my troubles placed on the scales
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
they would be heavier than the sand of the sea. That's why I spoke so rashly.
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
For the arrows of the Almighty are in me; their poison saps my spirit. God's terrors are lined up against me.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
Don't wild donkeys bray when their grass is gone? Don't cattle groan when they don't have food!
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
Can something that's tasteless be eaten without salt? Is there any taste in the white of an egg?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
I just can't touch any food—even the thought makes me feel sick!
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Oh, if only I could have what I really want, that God would give me what I most desire—
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
that God would be willing to crush me to death, that he would just let me die!
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
But it still comforts me to know, making me happy through the never-ending pain, that I have never rejected the words of God.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
Why should I go on waiting when I don't have the strength? Why should I keep going when I don't know what is going to happen to me?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
Am I as strong as rock? Am I made out of bronze?
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
How can I help myself now that any chance of success is ripped away from me?
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
Anyone who isn't kind to a friend has given up respecting the Almighty.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
My brothers have acted as deceptively as a desert stream, rushing waters in the desert that vanish.
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
The stream floods when it is full of dark ice and melting snow,
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
but in the heat it dries up and disappears, vanishing from where it once was.
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
Camel caravans turn aside to look for water, but don't find any and they die.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
Caravans from Tema looked, travelers from Sheba were confident,
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
but their hopes were dashed—they came and found nothing.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
Now you are no help, just like that—you see my trouble and you're afraid.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
Have I asked you for anything? Have I told you to bribe anyone for me from your wealth?
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
Have I asked you to rescue me from an enemy? Have I told you to save me from my oppressors?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Explain this to me, and I'll be quiet. Show me where I'm wrong.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
Honest words are painful, but what do your arguments prove?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
Are you going to argue over what I said, when the words of someone in despair should be left to blow away in the wind?
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
You would play dice to win an orphan; you would bargain away your friend!
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Look me in the eye and see if I'm lying to your face!
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Don't talk like this! Don't be unjust! What I'm saying is right.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
I'm not telling lies—don't you think I wouldn't know if I was wrong?”