< Ayuba 6 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
But Job answered, and said:
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
O that my sins, whereby I have deserved wrath, and the calamity that I suffer, were weighed in a balance.
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
As the sand of the sea this would appear heavier: therefore my words are full of sorrow:
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
For the arrows of the Lord are in me, the rage whereof drinketh up my spirit, and the terrors of the Lord war against me.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
Will the wild ass bray when he hath grass? or will the ox low when he standeth before a full manger?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
Or can an unsavoury thing be eaten, that is not seasoned with salt? or can a man taste that which when tasted bringeth death?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
The things which before my soul would not touch, now, through anguish are my meats.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Who will grant that my request may come: and that God may give me what I look for?
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
And that he that hath begun may destroy me, that he may let loose his hand, and cut me off?
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
And that this may be my comfort, that afflicting me with sorrow, he spare not, nor I contradict the words of the Holy One.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
For what is my strength, that I can hold out? or what is my end that I should keep patience?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
My strength is not the strength of stones, nor is my flesh of brass.
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
Behold there is no help for me in myself, and my familiar friends also are departed from me.
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
He that taketh away mercy from his friend, forsaketh the fear of the Lord.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
My brethren have passed by me, as the torrent that passeth swiftly in the valleys.
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
They that fear the hoary frost, the snow shall fall upon them.
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
At the time when they shall be scattered they shall perish: and after it groweth hot they shall be melted out of their place.
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
The paths of their steps are entangled: they shall walk in vain, and shall perish.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
Consider the paths of Thema, the ways of Saba, and wait a little while.
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
They are confounded, because I have hoped: they are come also even unto me, and are covered with shame.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
Now you are come: and now seeing my affliction you are afraid.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
Did I say: Bring to me, and give me of your substance?
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
Or deliver me from the hand of the enemy, and rescue me out of the hand of the mighty?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Teach me, and I will hold my peace: and if I have been ignorant in any thing, instruct me.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
Why have you detracted the words of truth, whereas there is none of you that can reprove me?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
You dress up speeches only to rebuke, and you utter words to the wind.
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
You rush in upon the fatherless, and you endeavour to overthrow your friend.
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
However finish what you have begun, give ear, and see whether I lie.
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Answer, I beseech you, without contention: and speaking that which is just, judge ye.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
And you shall not And iniquity in my tongue, neither shall folly sound in my mouth.