< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
And Job answered and said,
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
Oh that my grief were thoroughly weighed, and all my calamity laid in the balances!
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
For now it would be heavier than the sand of the seas; therefore my words are vehement.
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
For the arrows of the Almighty are within me, their poison drinketh up my spirit: the terrors of God are arrayed against me.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
Doth the wild ass bray by the grass? loweth an ox over his fodder?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
Shall that which is insipid be eaten without salt? Is there any taste in the white of an egg?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
What my soul refuseth to touch, that is as my loathsome food.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Oh that I might have my request, and that God would grant my desire!
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
And that it would please God to crush me, that he would let loose his hand and cut me off!
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
Then should I yet have comfort; and in the pain which spareth not I would rejoice that I have not denied the words of the Holy One.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
What is my strength, that I should hope? and what is mine end, that I should have patience?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
Is my strength the strength of stones? is my flesh of brass?
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
Is it not that there is no help in me, and soundness is driven away from me?
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
For him that is fainting kindness [is meet] from his friend; or he forsaketh the fear of the Almighty.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
My brethren have dealt deceitfully as a stream, as the channel of streams which pass away,
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
Which are turbid by reason of the ice, in which the snow hideth itself:
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
At the time they diminish, they are dried up; when heat affecteth them, they vanish from their place:
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
They wind about in the paths of their course, they go off into the waste and perish.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
The caravans of Tema looked, the companies of Sheba counted on them:
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
They are ashamed at their hope; they come thither, and are confounded.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
So now ye are nothing; ye see a terrible object and are afraid.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
Did I say, Bring unto me, and make me a present from your substance?
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
Or, rescue me from the hand of the oppressor, and redeem me from the hand of the violent?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Teach me, and I will hold my tongue; and cause me to understand wherein I have erred.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
How forcible are right words! but what doth your upbraiding reprove?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
Do ye imagine to reprove words? The speeches of one that is desperate are indeed for the wind.
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Yea, ye overwhelm the fatherless, and dig [a pit] for your friend.
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Now therefore if ye will, look upon me; and it shall be to your face if I lie.
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Return, I pray you, let there be no wrong; yea, return again, my righteousness shall be in it.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
Is there wrong in my tongue? cannot my taste discern mischievous things?

< Ayuba 6 >