< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Job antwoordde, en sprak:
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
Ach, mocht mijn wrevel worden gewogen, Maar tegelijk met mijn leed op de weegschaal gelegd:
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
Want omdat het zwaarder is dan het zand aan de zee, Daarom gingen ook mijn woorden de perken te buiten.
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
Ja, de pijlen van den Almachtige blijven in mij steken, Mijn geest zuigt er het gif van op; De verschrikkingen Gods Stellen zich tegen mij in slagorde op!
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
Balkt soms de woudezel bij het gras Of loeit het rund bij zijn kribbe?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
Kan het laffe zonder zout worden gegeten, Of is er smaak aan het wit van een ei?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
Neen, ik weiger, het aan te raken, Ze zijn voor mij een walgelijke spijs!
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Ach, dat mijn bede werd verhoord, En dat God mijn wens mocht vervullen;
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
Dat het God behaagde, mij te verpletteren, Zijn hand zich bewoog, om mij weg te maaien.
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
Dat zou een troost voor mij zijn, En ik danste ondanks mijn leed: "Hij spaart mij niet, Omdat ik den Heilige mijn wens niet verzweeg!".
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
Want wat is mijn kracht, dat ik nu nog zou wachten, Wat mijn uitzicht, dat ik langer zou leven?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
Is mijn kracht soms als die van een steen, Is mijn vlees soms van brons?
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
Ben ik niet geheel van redding verstoken, Is iedere hulp mij niet ontzegd?
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
Maar wie zijn vriend barmhartigheid weigert, Verzaakt de vrees voor den Almachtige!
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
Toch zijn mijn broeders als een beek onbetrouwbaar, Als een stortbeek, die wegstroomt:
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
Die bedekt zijn met ijs, Of bedolven onder sneeuw;
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
Zodra de hitte komt, drogen zij uit, Zodra het warm wordt, zijn ze verdwenen.
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
Ze buigen af van de weg, die ze gaan, En verliezen zich in de woestijn;
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
De karavanen van Tema zien er naar uit, De convooien van Sjeba hebben er hun hoop op gevestigd:
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
Maar ze worden in hun verwachting beschaamd, Staan bij hun aankomst te schande.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
Zo zijt gij voor mij nu geworden: Gij aanschouwt mijn ellende, en beangst deinst gij terug!
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
Heb ik gevraagd: Geeft mij iets ten geschenke, Of staat mij van uw vermogen iets af;
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
Of redt mij uit de hand van den vijand, Bevrijdt mij uit de greep der tyrannen?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Neen, onderricht mij, en dan zal ik zwijgen; Laat mij inzien, waarin ik heb gedwaald!
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
Hoe zoet zijn woorden, die oprecht zijn gemeend, Maar hoe grievend de berisping van u!
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
Meent gij, mijn woorden te moeten berispen: Woorden van een wanhopige, die in de wind zijn gesproken?
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Wilt gij het lot over een onschuldige werpen, En de staf breken over uw vriend?
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Welnu dan, wilt mij aanhoren: Ik lieg u toch niet in het gezicht.
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Bezint u, en laat er geen onrecht geschieden; Bezint u, mijn onschuld zal blijken!
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
Is er soms onrecht op mijn tong, Of kan mijn gehemelte de rampen niet proeven;

< Ayuba 6 >