< Ayuba 5 >
1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Ahora pues da voces, si habrá quien te responda; y si habrá alguno de los santos a quien mires.
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
Es cierto que al insensato la ira le mata; y al codicioso consume la envidia.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
Yo he visto al necio que echaba raíces, y en la misma hora maldije su habitación.
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
Sus hijos serán lejos de la salud, y en la puerta serán quebrantados, y no habrá quien los libre.
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
Hambrientos comerán su segada, y la sacarán de entre las espinas; y sedientos beberán su hacienda.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
Porque la pena no sale del polvo, ni la molestia reverdece de la tierra.
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
Antes como las centellas se levantan para volar por el aire, así el hombre nace para la aflicción.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
Ciertamente yo buscaría a Dios, y depositaría en él mis negocios;
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
El cual hace grandes cosas, que no hay quien las comprenda; y maravillas que no tienen cuento:
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
Que da la lluvia sobre la haz de la tierra, y envía las aguas sobre las haces de las plazas:
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
Que pone los humildes en altura, y los enlutados son levantados a salud:
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
Que frustra los pensamientos de los astutos, para que sus manos no hagan nada:
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
Que prende a los sabios en su astucia, y el consejo de los perversos es entontecido.
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
De día se topan con tinieblas, y en mitad del día andan a tiento, como en noche.
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
Y libra de la espada al pobre, de la boca de los impíos, y de la mano violenta.
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
Que es esperanza al menesteroso, y la iniquidad cerró su boca.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
He aquí, que bienaventurado es el hombre a quien Dios castiga: por tanto no menosprecies la corrección del Todopoderoso.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
Porque él es el que hace la llaga, y él que la ligará: el hiere, y sus manos curan.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
En seis tribulaciones te librará, y en la séptima no te tocará el mal.
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
En la hambre te redimirá de la muerte, y en la guerra, de las manos de la espada.
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Del azote de la lengua serás encubierto: ni temerás de la destrucción, cuando viniere.
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
De la destrucción y de la hambre te reirás, y no temerás de las bestias del campo.
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
Y aun con las piedras del campo tendrás tu concierto, y las bestias del campo te serán pacíficas.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
Y sabrás que hay paz en tu tienda; y visitarás tu morada, y no pecarás.
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Y entenderás que tu simiente es mucha; y tus pimpollos, como la yerba de la tierra.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Y vendrás en la vejez a la sepultura, como el montón de trigo que se coge a su tiempo.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
He aquí lo que hemos inquirido, lo cual es así: óyelo, y tú sabe para ti.