< Ayuba 5 >

1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Rufe doch! Ist einer, der dir antwortet? Und an welchen von den Heiligen willst du dich wenden?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
Denn den Toren erwürgt der Zorn, und den Einfältigen tötet der Eifer.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
Ich selbst habe einen Toren gesehen, der Wurzel schlug; sobald ich aber sein Gehöft verfluchte,
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
waren seine Söhne vom Glück verlassen und wurden unterdrückt im Tore, und niemand rettete sie;
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
seine Ernte fraß der Hungrige und nahm sie ihm aus den Dornen heraus, und sein Vermögen schnappten die Habgierigen weg.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
Denn Unglück wächst nicht aus dem Staub hervor, und Unheil sproßt nicht aus der Erde;
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
sondern der Mensch ist zum Unglück geboren, wie die Funken aufwärts fliegen.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
Aber doch würde ich Gott suchen und meine Rede an ihn richten,
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
der große, unerforschliche Dinge tut, Wunder ohne Zahl:
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
Er gießt Regen auf die Erde und sendet Wasser über die Fluren;
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
er erhöht die Niedrigen und die Leidtragenden erlangen das Heil;
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
er vereitelt die Anschläge der Listigen, daß ihre Hand nicht helfen kann;
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
er fängt die Weisen in ihrer Klugheit, und der Verschmitzten Rat überstürzt sich selbst;
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
bei Tage stoßen sie an wie im Dunkel und tappen zu Mittag wie in der Nacht.
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
Aber den Armen errettet er vom Schwert und aus ihrem Maul und den Bedürftigen aus der Hand des Starken,
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
daß der Geringe Hoffnung faßt und die Frechheit ihr Maul verschließt.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Siehe, wohl dem Menschen, den Gott straft! Darum verwirf die Züchtigung des Allmächtigen nicht!
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
Denn er verwundet und verbindet, er zerschlägt und seine Hand heilt.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
In sechs Trübsalen wird er dich erretten, und in sieben wird dich kein Leid berühren:
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
In Hungersnot wird er dich vom Tode erlösen und im Kriege von dem Schwert;
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
vor der Geißel der Zunge wirst du geborgen sein und wirst Gewalttätigkeit nicht fürchten, wenn sie kommt;
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
der Verwüstung und Dürre wirst du lachen und vor den wilden Tieren nicht erschrecken;
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
denn mit den Steinen des Feldes stehst du im Bunde, und die Tiere des Feldes halten Frieden mit dir.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
Du wirst erfahren, daß dein Zelt sicher ist, und untersuchst du deine Wohnung, so fehlt dir nichts.
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Du wirst erfahren, daß dein Same zahlreich wird und deine Sprößlinge wie das Gras auf Erden.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Du wirst in gutem Alter begraben werden, wie man Garben einbringt zu ihrer Zeit.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Siehe, das haben wir erforscht, so ist es; vernimm es und merke es dir wohl!

< Ayuba 5 >