< Ayuba 5 >

1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Rufe doch! was gilts, ob einer dir antworte? Und an welchen von den Heiligen willst du dich wenden?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
Einen Toren aber erwürgt wohl der Unmut, und den Unverständigen tötet der Eifer.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
Ich sah einen Toren eingewurzelt, und ich fluchte plötzlich seinem Hause.
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
Seine Kinder werden fern sein vom Heil und werden zerschlagen werden im Tor, da kein Erretter sein wird.
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
Seine Ernte wird essen der Hungrige und auch aus den Hecken sie holen, und sein Gut werden die Durstigen aussaufen.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
Denn Mühsal aus der Erde nicht geht und Unglück aus dem Acker nicht wächst;
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
sondern der Mensch wird zu Unglück geboren, wie die Vögel schweben, emporzufliegen.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
Ich aber würde zu Gott mich wenden und meine Sache vor ihn bringen,
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
der große Dinge tut, die nicht zu erforschen sind, und Wunder, die nicht zu zählen sind:
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
der den Regen aufs Land gibt und läßt Wasser kommen auf die Gefilde;
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
der die Niedrigen erhöht und den Betrübten emporhilft.
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
Er macht zunichte die Anschläge der Listigen, daß es ihre Hand nicht ausführen kann;
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
er fängt die Weisen in ihrer Listigkeit und stürzt der Verkehrten Rat,
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
daß sie des Tages in der Finsternis laufen und tappen am Mittag wie in der Nacht.
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
Er hilft den Armen von dem Schwert, von ihrem Munde und von der Hand des Mächtigen,
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
und ist des Armen Hoffnung, daß die Bosheit wird ihren Mund müssen zuhalten.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Siehe, selig ist der Mensch, den Gott straft; darum weigere dich der Züchtigung des Allmächtigen nicht.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
Denn er verletzt und verbindet; er zerschlägt und seine Hand heilt.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
Aus sechs Trübsalen wird er dich erretten, und in der siebenten wird dich kein Übel rühren:
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
in der Teuerung wird er dich vom Tod erlösen und im Kriege von des Schwertes Hand;
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Er wird dich verbergen vor der Geißel Zunge, daß du dich nicht fürchtest vor dem Verderben, wenn es kommt;
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
im Verderben und im Hunger wirst du lachen und dich vor den wilden Tieren im Lande nicht fürchten;
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
sondern sein Bund wird sein mit den Steinen auf dem Felde, und die wilden Tiere im Lande werden Frieden mit dir halten.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
Und du wirst erfahren, daß deine Hütte Frieden hat, und wirst deine Behausung versorgen und nichts vermissen,
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
und wirst erfahren, daß deines Samens wird viel werden und deine Nachkommen wie das Gras auf Erden,
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
und wirst im Alter zum Grab kommen, wie Garben eingeführt werden zu seiner Zeit.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Siehe, das haben wir erforscht und ist also; dem gehorche und merke du dir's.

< Ayuba 5 >