< Ayuba 5 >
1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Crie maintenant! Y aura-t-il quelqu'un qui te réponde? Et vers lequel des saints te tourneras-tu?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
La colère tue l'insensé, et le dépit fait mourir celui qui est destitué de sens;
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
J'ai vu l'insensé étendant ses racines, mais soudain j'ai maudit sa demeure.
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
Ses fils sont loin de tout secours, ils sont écrasés à la porte, et personne ne les délivre;
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
L'affamé dévore sa moisson; il la lui prend à travers les épines de sa haie; l'homme altéré convoite ses biens.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
Car la souffrance ne sort pas de la poussière, et la peine ne germe pas du sol,
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
De sorte que l'homme soit né pour la peine, comme l'étincelle pour voler en haut.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
Mais moi, j'aurais recours à Dieu, et j'adresserais ma parole à Dieu,
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
Qui fait de grandes choses qu'on ne peut sonder, de merveilleuses choses qu'on ne peut compter;
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
Qui répand la pluie sur la face de la terre, et qui envoie les eaux sur la face des champs;
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
Qui met en haut ceux qui sont abaissés, et ceux qui sont en deuil au faîte du bonheur;
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
Qui dissipe les projets des hommes rusés, et leurs mains ne viennent à bout de rien;
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
Qui prend les sages dans leurs propres ruses, et le dessein des pervers est renversé.
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
De jour, ils rencontrent les ténèbres, et, comme dans la nuit, ils tâtonnent en plein midi;
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
Et il délivre le pauvre de l'épée de leur bouche, et de la main des puissants.
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
Et il y a une espérance pour les malheureux, et la méchanceté a la bouche fermée.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Voici, heureux l'homme que Dieu châtie! Ne méprise donc pas la correction du Tout-Puissant.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
Car c'est lui qui fait la plaie et la bande; il blesse et ses mains guérissent.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
Dans six détresses, il te délivrera; et dans sept, le mal ne te touchera point.
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
En temps de famine, il te garantira de la mort, et en temps de guerre, du tranchant de l'épée.
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Tu seras à couvert du fléau de la langue, et tu n'auras point peur de la désolation, quand elle arrivera.
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
Tu riras de la dévastation et de la famine, et tu n'auras pas peur des bêtes de la terre;
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
Car tu auras un pacte avec les pierres des champs, et les bêtes des champs seront en paix avec toi.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
Et tu verras la prospérité dans ta tente: tu visiteras tes pâturages,
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Et rien ne t'y manquera; et tu verras ta postérité croissante, et tes descendants pareils à l'herbe de la terre.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Tu entreras mûr dans le tombeau, comme une gerbe qu'on emporte en son temps.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Voilà, nous avons examiné la chose; elle est ainsi, écoute cela, et fais-en ton profit.