< Ayuba 5 >

1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Crie maintenant; y aura-t-il quelqu'un qui te réponde? et vers qui d'entre les saints te tourneras-tu?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
Certainement la colère tue le fou, et le dépit fait mourir le sot.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
J'ai vu le fou qui s'enracinait, mais j'ai aussitôt maudit sa demeure.
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
Ses enfants, bien loin de trouver de la sûreté, sont écrasés aux portes, et personne ne les délivre.
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
Sa moisson est dévorée par l'affamé, qui même la ravit d'entre les épines; et le voleur engloutit leurs biens.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
Or le tourment ne sort pas de la poussière, et le travail ne germe pas de la terre;
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
Quoique l'homme naisse pour être agité, comme les étincelles pour voler en haut.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
Mais moi, j'aurais recours au [Dieu] Fort, et j'adresserais mes paroles à Dieu,
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
Qui fait des choses si grandes qu'on ne les peut sonder, [et] tant de choses merveilleuses, qu'il est impossible de les compter.
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
Qui répand la pluie sur la face de la terre, et qui envoie les eaux sur les campagnes.
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
Qui élève ceux qui sont bas, et qui fait que ceux qui sont en deuil sont en sûreté dans une haute retraite.
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
Il dissipe les pensées des hommes rusés, de sorte qu'ils ne viennent point à bout de leurs entreprises.
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
Il surprend les sages en leur ruse, et le conseil des méchants est renversé.
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
De jour ils rencontrent les ténèbres, et ils marchent à tâtons en plein midi, comme dans la nuit.
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
Mais il délivre le pauvre de [leur] épée, de leur bouche, et de la main de l'homme puissant.
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
Ainsi il arrive au pauvre ce qu'il a espéré, mais l'iniquité a la bouche fermée.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Voilà, ô que bienheureux est celui que Dieu châtie! ne rejette donc point le châtiment du Tout-puissant.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
Car c'est lui qui fait la plaie, et qui la bande; il blesse, et ses mains guérissent.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
Il te délivrera dans six afflictions, et à la septième le mal ne te touchera point.
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
En temps de famine il te garantira de la mort, et en temps de guerre [il te préservera] de l'épée.
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Tu seras à couvert du fléau de la langue, et tu n'auras point peur du pillage quand il arrivera;
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
Tu riras durant le pillage et durant la famine, et tu n'auras point peur des bêtes sauvages.
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
Même tu feras accord avec les pierres des champs, tu seras en paix avec les bêtes sauvages.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
Tu connaîtras que la prospérité sera dans ta tente; tu pourvoiras à ta demeure, et tu n'y seras point trompé.
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Et tu verras croître ta postérité et tes descendants, comme l'herbe de la terre.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Tu entreras au sépulcre en vieillesse, comme un monceau de gerbes s'entasse en sa saison.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Voilà, nous avons examiné cela, et il est ainsi; écoute-le, et le sache pour ton bien.

< Ayuba 5 >