< Ayuba 5 >

1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Crie donc! Y a-t-il quelqu’un qui te réponde? Et vers lequel des saints te tourneras-tu?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
Car le chagrin fait mourir le sot, et la jalousie tue le simple.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
J’ai vu le sot s’enraciner, et soudain j’ai maudit sa demeure;
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
Ses fils sont loin de la sûreté, et sont écrasés dans la porte, et il n’y a personne pour délivrer;
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
Sa moisson, l’affamé la mange, et jusque parmi les épines il la prend; et le piège guette son bien.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
Car l’affliction ne sort pas de la poussière, et la misère ne germe pas du sol;
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
Car l’homme est né pour la misère, comme les étincelles volent en haut.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
Mais moi je rechercherai Dieu, et devant Dieu je placerai ma cause, –
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
Qui fait de grandes choses qu’on ne peut sonder, des merveilles à ne pouvoir les compter;
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
Qui donne la pluie sur la face de la terre, et envoie des eaux sur la face des campagnes,
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
Plaçant en haut ceux qui sont abaissés; et ceux qui sont en deuil sont élevés au bonheur.
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
Il dissipe les projets des hommes rusés, et leurs mains n’accomplissent pas leurs conseils.
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
Il prend les sages dans leur ruse, et le conseil des astucieux est précipité:
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
De jour, ils rencontrent les ténèbres, et en plein midi ils marchent à tâtons, comme de nuit.
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
Et il sauve le pauvre de l’épée, de leur bouche, et de la main du fort;
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
Et il arrive au chétif ce qu’il espère, et l’iniquité a la bouche fermée.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Voici, bienheureux l’homme que Dieu reprend! Ne méprise donc pas le châtiment du Tout-puissant.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
Car c’est lui qui fait la plaie et qui la bande; il frappe, et ses mains guérissent.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
En six détresses il te délivrera, et, dans sept, le mal ne t’atteindra pas.
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
Dans la famine il te délivrera de la mort, et, dans la guerre, de la puissance de l’épée.
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Tu seras à couvert du fouet de la langue, et tu ne craindras pas le désastre quand il viendra.
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
Tu te riras du désastre et de la faim, et tu n’auras pas peur des bêtes de la terre;
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
Car tu auras une alliance avec les pierres des champs, et les bêtes des champs seront en paix avec toi.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
Tu sauras que ta tente est prospère, tu visiteras ta demeure et tu n’y trouveras rien qui manque,
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Et tu sauras que ta postérité est nombreuse, et tes rejetons, comme l’herbe de la terre.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Tu entreras au sépulcre en bonne vieillesse, comme on enlève le tas de gerbes en sa saison.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Voici, nous avons examiné cela; il en est ainsi. Écoute-le, et sache-le pour toi-même.

< Ayuba 5 >