< Ayuba 5 >
1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Call now; is there any that will answer thee? and to which of the holy ones wilt thou turn?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
For vexation killeth the foolish man, and jealousy slayeth the silly one.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
I have seen the foolish taking root: but suddenly I cursed his habitation.
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
His children are far from safety, and they are crushed in the gate, neither is there any to deliver them.
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
Whose harvest the hungry eateth up, and taketh it even out of the thorns, and the snare gapeth for their substance.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
For affliction cometh not forth of the dust, neither doth trouble spring out of the ground;
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
But man is born unto trouble, as the sparks fly upward.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
But as for me, I would seek unto God, and unto God would I commit my cause:
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
Which doeth great things and unsearchable; marvelous things without number:
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
Who giveth rain upon the earth, and sendeth waters upon the fields:
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
So that he setteth up on high those that be low; and those which mourn are exalted to safety.
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
He frustrateth the devices of the crafty, so that their hands cannot perform their enterprise.
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
He taketh the wise in their own craftiness: and the counsel of the froward is carried headlong.
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
They meet with darkness in the daytime, and grope at noonday as in the night.
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
But he saveth from the sword of their mouth, even the needy from the hand of the mighty.
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
So the poor hath hope, and iniquity stoppeth her mouth.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Behold, happy is the man whom God correcteth: therefore despise not thou the chastening of the Almighty.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
For he maketh sore, and bindeth up; he woundeth, and his hands make whole.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
He shall deliver thee in six troubles; yea, in seven there shall no evil touch thee.
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
In famine he shall redeem thee from death; and in war from the power of the sword.
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Thou shalt be hid from the scourge of the tongue; neither shalt thou be afraid of destruction when it cometh.
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
At destruction and dearth thou shalt laugh; neither shalt thou be afraid of the beasts of the earth.
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
For thou shalt be in league with the stones of the field; and the beasts of the field shall be at peace with thee.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
And thou shalt know that thy tent is in peace; and thou shalt visit thy fold, and shalt miss nothing.
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Thou shalt know also that thy seed shall be great, and thine offspring as the grass of the earth.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Thou shalt come to thy grave in a full age, like as a shock of corn cometh in in its season.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Lo this, we have searched it, so it is; hear it, and know thou it for thy good.