< Ayuba 5 >

1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Do but call: is there one that will answer thee? and to whom of the saints wilt thou turn thyself?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
For vexation will prove death to a foolish man, and jealousy will slay the simple.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
I have myself seen the foolish taking root; but I suddenly held his habitation as accursed.
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
His children are far from help, and men crush them in the gate, with no one to deliver them.
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
[He it is] whose harvest the hungry eateth up, and taketh it even out of the thorns, and the robber snatcheth eagerly after their substance.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
For wrong doth not come forth out of the dust, neither doth trouble grow up out of the ground;
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
But man is born unto trouble, as young birds take up their flight.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
I, however, would have besought God, and unto God would I have committed my cause;
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
Who doth great things which are unsearchable, marvelous things till they are without number;
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
Who giveth rain upon the surface of the earth, and sendeth out waters over the face of the fields;
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
To set up the lowly on high, that those who mourn may rise high to happiness;
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
[But] who frustrateth the plans of the crafty, so that their hands cannot execute their well-devised counsel;
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
Who catcheth the wise in their own craftiness; and the advise of the perverse is hastened on headlong;
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
By day they meet with darkness, and as though it were night they grope about in the noon of day;
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
But who saveth from the sword, from their mouth, and from the hand of the mighty, the needy one:
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
And so cometh to the indigent hope, and iniquity stoppeth her mouth.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Behold, happy is the man whom God admonisheth: despise then not the correction of the Almighty.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
For he it is that woundeth, and bindeth up: he smiteth, and his hands do heal.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
In six distresses will he deliver thee; and in seven there shall no evil touch thee.
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
In famine he redeemeth thee from death; and in war from the power of the sword.
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Against the scourge of the tongue shall thou he hidden; and thou needest not be afraid of destruction when it cometh.
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
At destruction and famine canst thou laugh; and thou needest not have any fear of the beasts of the earth.
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
For with the stones of the field shalt thou have thy covenant; and the beasts of the field shall be at peace with thee.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
And thou shalt know that there is peace in thy tent; and thou wilt look over thy habitation, and shalt miss nothing.
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
And thou shalt know that thy seed is numerous, and thy offspring as the herbage of the earth.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Thon wilt go in a ripe age unto the grave, as a shock of corn is carried home in its season.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Behold this, we have searched it out, so it is: hear it, and do thou note it well for thyself.

< Ayuba 5 >