< Ayuba 5 >

1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Call nowe, if any will answere thee, and to which of the Saintes wilt thou turne?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
Doubtlesse anger killeth the foolish, and enuie slayeth the idiote.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
I haue seene the foolish well rooted, and suddenly I cursed his habitation, saying,
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
His children shalbe farre from saluation, and they shall be destroyed in the gate, and none shall deliuer them.
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
The hungrie shall eate vp his haruest: yea, they shall take it from among the thornes, and the thirstie shall drinke vp their substance.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
For miserie commeth not foorth of the dust, neither doeth affliction spring out of the earth.
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
But man is borne vnto trauaile, as the sparkes flie vpwarde.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
But I would inquire at God, and turne my talke vnto God:
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
Which doeth great things and vnsearchable, and marueilous things without nomber.
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
He giueth raine vpon the earth, and powreth water vpon the streetes,
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
And setteth vp on hie them that be lowe, that the sorowfull may be exalted to saluation.
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
He scattereth the deuices of the craftie: so that their handes can not accomplish that which they doe enterprise.
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
He taketh the wise in their craftinesse, and the counsel of the wicked is made foolish.
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
They meete with darkenesse in the day time, and grope at noone day, as in the night.
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
But he saueth the poore from the sword, from their mouth, and from the hande of the violent man,
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
So that the poore hath his hope, but iniquitie shall stop her mouth.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Beholde, blessed is the man whome God correcteth: therefore refuse not thou the chastising of the Almightie.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
For he maketh the wound, and bindeth it vp: he smiteth, and his handes make whole.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
He shall deliuer thee in sixe troubles, and in the seuenth the euill shall not touch thee.
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
In famine he shall deliuer thee from death: and in battel from the power of the sworde.
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Thou shalt be hid from the scourge of the tongue, and thou shalt not be afraid of destruction when it commeth.
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
But thou shalt laugh at destruction and dearth, and shalt not be afraide of the beast of the earth.
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
For the stones of the fielde shall be in league with thee, and the beastes of the field shall be at peace with thee.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
And thou shalt knowe, that peace shall be in thy tabernacle, and thou shalt visite thine habitation, and shalt not sinne.
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Thou shalt perceiue also, that thy seede shalbe great, and thy posteritie as the grasse of the earth.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Thou shalt goe to thy graue in a ful age, as a ricke of corne commeth in due season into the barne.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Lo, thus haue we inquired of it, and so it is: heare this and knowe it for thy selfe.

< Ayuba 5 >