< Ayuba 5 >

1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Call now, is there any who will answer thee? And to which of the holy ones will thou turn?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
For vexation kills the foolish man, and jealousy slays the silly one.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
I have seen the foolish taking root, but suddenly I cursed his habitation.
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
His sons are far from safety, and they are crushed in the gate. Neither is there any to deliver them,
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
whose harvest the hungry eat up, and takes it even out of the thorns, and the snare gapes for their substance.
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
For affliction does not come forth from the dust, nor does trouble spring out of the ground,
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
but man is born to trouble, as the sparks fly upward.
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
But as for me, I would seek to God. And to God I would commit my cause,
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
who does great things and unsearchable, marvelous things without number,
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
who gives rain upon the earth, and sends waters upon the fields,
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
so that he sets up on high those who are low, and those who mourn are exalted to safety.
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
He frustrates the devices of the crafty so that their hands cannot perform their enterprise.
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
He takes the wise in their own craftiness, and the counsel of the cunning is carried headlong.
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
They meet with darkness in the daytime, and grope at noonday as in the night.
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
But he saves from the sword of their mouth, even the needy from the hand of the mighty.
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
So a poor man has hope, and iniquity stops her mouth.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Behold, happy is the man whom God corrects. Therefore do not despise thou the chastening of the Almighty.
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
For he injures, and binds up. He wounds, and his hands make whole.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
He will deliver thee in six troubles. Yea, in seven there shall no evil touch thee.
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
In famine he will redeem thee from death, and in war from the power of the sword.
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Thou shall be hid from the scourge of the tongue. Neither shall thou be afraid of destruction when it comes.
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
At destruction and dearth thou shall laugh, nor shall thou be afraid of the beasts of the earth.
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
For thou shall be in league with the stones of the field, and the beasts of the field shall be at peace with thee.
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
And thou shall know that thy tent is in peace, and thou shall visit thy fold, and shall miss nothing.
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Thou shall know also that thy seed shall be great, and thine offspring as the grass of the earth.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Thou shall come to thy grave in a full age, like a shock of grain comes in its season.
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Lo this, we have searched it, so it is. Hear it, and know thou it for thy good.

< Ayuba 5 >