< Ayuba 5 >

1 “Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
Roep maar: er is niemand, die u antwoord geeft; Tot wien van de heiligen wilt ge u wenden?
2 Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
Het is dus de wrevel, die den dwaas vermoordt, De gramschap doodt dus den zot.
3 Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
Ik heb den dwaas wel wortel zien schieten, Maar plotseling verrotte zijn akker;
4 ’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
Zijn kinderen werden van hulp verstoken, Reddeloos vertrapt in de poort;
5 mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
Wat zij hebben geoogst, eet een hongerige op, En de dorstige rooft en drinkt de melk van hun kudde
6 Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
Want het kwaad schiet niet op uit het stof, En de rampspoed ontspruit uit de aarde niet:
7 Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
Maar het is de mens, die zichzelf de rampspoed verwekt, Zoals de vonken naar boven spatten!
8 “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
Ik, ik wend mij tot God, En leg mijn zaak aan de Godheid voor:
9 Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
Hij, die grootse en ondoorgrondelijke dingen wrocht En ontelbare wonderen;
10 Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
Die regen over de aarde zendt, En water over de velden giet;
11 Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
Die de nederigen op de hoogte verheft, En treurenden het hoogste geluk doet smaken.
12 Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
Die de plannen der sluwen verijdelt, Zodat hun handen de ontwerpen niet ten uitvoer brengen;
13 Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
Die de wijzen vangt in hun eigen list, Zodat de toeleg der slimmen mislukt,
14 Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
En midden op de dag zij op duisternis stuiten, En rondtasten op klaarlichte dag, zoals in de nacht;
15 Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
Maar die de geplaagden redt uit hun hand, Den arme uit de greep van den sterke:
16 Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
Zodat er weer hoop voor den zwakke is, En het onrecht de mond sluit.
17 “Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
Gelukkig, gij mens, dien God kastijdt: Versmaad dus de straf van den Almachtige niet!
18 Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
Want Hij wondt, maar verbindt, Hij kwetst, maar zijn handen genezen.
19 Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
Uit zes noden zal Hij u redden, En in de zevende treft u geen kwaad:
20 Lokacin yunwa yana tsare ka daga mutuwa, a cikin yaƙi kuma yana kāre ka daga sarar takobi.
In hongersnood redt Hij u van de dood, In de oorlog uit de greep van het zwaard;
21 Zai kāre ka daga ɓata suna, kuma ba ka bukata ka ji tsoro in hallaka ta zo.
Gij zijt veilig voor de gesel der tong, Zonder vrees voor het dreigend geweld.
22 Za ka yi wa hallaka da yunwa dariya; kuma ba ka bukata ka ji tsoron manyan namun jeji.
Met geweld en gebrek zult ge lachen, Voor wilde beesten niet vrezen:
23 Gama za ka zauna lafiya da duwatsu a gonaki, kuma manyan namun jeji za su yi zaman salama da kai.
Want ge hebt een verbond met de stenen op het veld, En het wild gedierte leeft in vriendschap met u
24 Za ka zauna lafiya a cikin tenti naka, za ka ƙirga kayanka za ka samu kome na nan.
Dan weet ge, dat uw tent in vrede is, Ge niets vermist, als ge uw woning doorzoekt;
25 Za ka san cewa’ya’yanka za su zama da yawa, zuriyarka kuma kamar ciyawa a ƙasa.
Dan weet ge, dat uw nageslacht talrijk zal zijn, Uw spruiten als het gras op het veld.
26 Za ka yi kyakkyawan tsufa kafin ka mutu, kamar yadda ake tara dammuna a lokacin girbi.
Eerst in uw ouderdom daalt ge ten grave, Zoals de schoof wordt binnengehaald, als het tijd is!
27 “Mun yi nazarin wannan, kuma gaskiya ne. Saboda haka ka ji, ka kuma yi amfani da shi.”
Zie, dit hebben we nagespeurd, en zó is het; Luister er naar, en neem het ter harte!

< Ayuba 5 >