< Ayuba 42 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Отвещав же Иов, рече ко Господу:
2 “Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
вем, яко вся можеши, невозможно же Тебе ничтоже.
3 Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
Кто есть таяй от Тебе совет, щадяй же словеса и от Тебе мнится утаити? Кто же возвестит ми, ихже не ведех, велия и дивная, ихже не знах?
4 “Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
Послушай же мене, Господи, да и аз возглаголю: вопрошу же Тя, ты же мя научи:
5 Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
слухом убо уха слышах Тя первее, ныне же око мое виде Тя:
6 Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
темже укорих себе сам, и истаях, и мню себе землю и пепел.
7 Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
Бысть же егда изглагола Господь вся глаголголы сия Иову, рече Господь ко Елифазу Феманитину: согрешил еси ты и оба друзие твои: не глаголасте бо предо Мною ничтоже истинно, якоже раб Мои Иов:
8 Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
ныне же возмите седмь телцев и седмь овнов и идите ко рабу Моему Иову, и сотворит жертву о вас: Иов же раб Мой помолится о вас, понеже точию лице его прииму: аще бо не его ради, погубил бых убо вас: не глаголасте бо истины на раба Моего Иова.
9 Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
Отиде же Елифаз Феманитин и Валдад Савхейский и Софар Минейский и сотвориша, якоже повеле им Господь. И отпусти грехи им Иова ради.
10 Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
Господь же возрасти Иова: молящуся же ему и о друзех своих, отпусти им грехи их, и даде Господь сугубая, елика бяху прежде Иову во усугубление.
11 Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
Услышаша же вси братия его и сестры его вся случившаяся ему, и приидоша к нему, и вси елицы знаху его первее: ядше же и пивше у него, утешиша его и дивишася о всех, яже наведе нань Бог: даде же ему кийждо агницу едину и четыре драхмы злата назнаменована.
12 Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
Господь же благослови последняя Иовля, неже прежняя: бяху же скоти его, овец четыренадесять тысящ, велблюдов шесть тысящ, супруг волов тысяща, ослиц стадных тысяща.
13 Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
Родишажеся ему сынове седмь и дщери три:
14 ’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
и нарече первую убо День, вторую же Кассию, третию же Амалфеев Рог:
15 Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
и не обретошася подобны в лепоте дщерем Иовлевым в поднебесней: даде же им отец наследие в братии их.
16 Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
Поживе же Иов по язве лет сто седмьдесят, всех же лет поживе двести четыредесять осмь. И виде Иов сыны своя и сыны сынов своих, даже до четвертаго рода.
17 Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.
И скончася Иов стар и исполнь дний.