< Ayuba 42 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Alors Job répondit à l'Éternel, et dit:
2 “Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
Je sais que tu peux tout, et qu'on ne saurait t'empêcher d'accomplir un dessein.
3 Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
“Qui obscurcit mes plans sans science? “J'ai parlé et je ne comprenais pas; ce sont des choses trop merveilleuses pour moi, et je ne les connais point.
4 “Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
“Écoute donc et je parlerai; je t'interrogerai et tu m'instruiras. “
5 Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
Mes oreilles avaient entendu parler de toi; mais, maintenant, mon œil t'a vu.
6 Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
C'est pourquoi je me condamne et je me repens, sur la poussière et sur la cendre.
7 Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
Or, après que l'Éternel eut ainsi parlé à Job, il dit à Éliphaz, de Théman: Ma colère est enflammée contre toi et contre tes deux amis, parce que vous n'avez pas parlé avec droiture devant moi, comme Job, mon serviteur.
8 Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
Maintenant, prenez sept taureaux et sept béliers, et allez vers mon serviteur Job, offrez un holocauste pour vous, et Job, mon serviteur, priera pour vous; et par égard pour lui, je ne vous traiterai pas selon votre folie, car vous n'avez pas parlé avec droiture devant moi, comme mon serviteur Job.
9 Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
Et Éliphaz, de Théman, Bildad, de Shuach, et Tsophar, de Naama, allèrent et firent comme leur avait dit l'Éternel, et l'Éternel eut égard à Job.
10 Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
Et l'Éternel rétablit Job dans ses biens, quand il eut prié pour ses amis; et il lui rendit au double tout ce qu'il avait eu.
11 Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
Tous ses frères, et toutes ses sœurs, tous ceux qui l'avaient connu auparavant vinrent vers lui, et mangèrent avec lui dans sa maison. Ils lui firent leurs condoléances, et le consolèrent au sujet de tout le mal que l'Éternel avait fait venir sur lui, et chacun lui donna une késita et un anneau d'or.
12 Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
Ainsi l'Éternel bénit le dernier état de Job plus que le premier; il eut quatorze mille brebis, six mille chameaux, et mille couples de bœufs, et mille ânesses.
13 Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
Il eut sept fils et trois filles.
14 ’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
Il donna à la première le nom de Jémima (colombe), à la seconde celui de Ketsia (parfum), à la troisième celui de Kéren-Happuc (flacon de fard).
15 Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
Et il ne se trouvait pas de femmes aussi belles que les filles de Job dans tout le pays; et leur père leur donna un héritage avec leurs frères.
16 Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
Job vécut, après ces choses, cent quarante ans, et vit ses fils et les fils de ses fils jusqu'à la quatrième génération.
17 Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.
Et il mourut âgé et rassasié de jours.

< Ayuba 42 >