< Ayuba 42 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Forsothe Joob answeride to the Lord, and seide,
2 “Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
Y woot, that thou maist alle thingis, and no thouyt is hid fro thee.
3 Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
Who is this, that helith counsel with out kunnyng? Therfor Y spak vnwiseli, and tho thingis that passiden ouer mesure my kunnyng.
4 “Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
Here thou, and Y schal speke; Y schal axe thee, and answere thou to me.
5 Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
Bi heryng of eere Y herde thee, but now myn iye seeth thee.
6 Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
Therfor Y repreue me, and do penaunce in deed sparcle and aische.
7 Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
Forsothe aftir that the Lord spak these wordis to Joob, he seide to Eliphat Themanytes, My stronge veniaunce is wrooth ayens thee, and ayens thi twey frendis; for ye `spaken not bifor me riytful thing, as my seruaunt Joob dide.
8 Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
Therfor take ye to you seuene bolis, and seuene rammes; and go ye to my seruaunt Joob, and offre ye brent sacrifice for you. Forsothe Joob, my seruaunt, schal preie for you; Y schal resseyue his face, that foli be not arettid to you; for ye `spaken not bifor me riytful thing, as my seruaunt Joob dide.
9 Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
Therfor Eliphat Themanytes, and Baldach Suythes, and Sophar Naamathites, yeden, and diden, as the Lord hedde spoke to hem; and the Lord resseyuede the face of Joob.
10 Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
Also the Lord was conuertid to the penaunce of Joob, whanne he preiede for hise frendis. And the Lord addide alle thingis double, whiche euere weren of Joob.
11 Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
Sotheli alle hise britheren, and alle hise sistris, and alle that knewen hym bifore, camen to hym; and thei eeten breed with hym in his hows, and moueden the heed on hym; and thei coumfortiden hym of al the yuel, which the Lord hadde brouyt in on hym; and thei yauen to hym ech man o scheep, and o goldun eere ring.
12 Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
Forsothe the Lord blesside the laste thingis of Joob, more than the bigynnyng of hym; and fouretene thousynde of scheep weren maad to hym, and sixe thousinde of camels, and a thousynde yockis of oxis, and a thousynde femal assis.
13 Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
And he hadde seuene sones, and thre douytris;
14 ’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
and he clepide the name of o douytir Dai, and the name of the secounde douytir Cassia, and the name of the thridde douytir `An horn of wymmens oynement.
15 Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
`Sotheli no wymmen weren foundun so faire in al erthe, as the douytris of Joob; and her fadir yaf eritage to hem among her britheren.
16 Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
Forsothe Joob lyuede aftir these betyngis an hundrid and fourti yeer, and `siy hise sones, and the sones of hise sones, `til to the fourthe generacioun;
17 Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.
and he was deed eld, and ful of daies.

< Ayuba 42 >