< Ayuba 42 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Then Job responded to Yahweh, and said: —
2 “Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
I know that, all things, thou canst do, and that no purpose can be withholden from thee.
3 Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
Who is it that hideth counsel without knowledge? Therefore, have I declared, but not understood, things too wonderful for me, which I could not know.
4 “Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
Hear thou, I pray thee, and, I, will speak, I will ask thee, and inform thou me.
5 Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
By the hearing of the ear, had I heard thee, but, now, mine own eye, hath seen thee.
6 Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
For this cause, I tremble and repent, on dust and ashes.
7 Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
And it came to pass, after Yahweh had spoken these words unto Job, that Yahweh, said unto Eliphaz the Temanite, Kindled is mine anger against thee and against thy two friends, for ye have not spoken concerning me the thing that is right, like my servant Job.
8 Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
Now, therefore, take unto you seven bullocks and seven rams, and go unto my servant Job, and ye shall offer up an ascending-sacrifice in your own behalf, and, Job my servant, shall pray over you, —for, him, will I accept, that I may not deal out to you disgrace, because ye have not spoken concerning me the thing that is right, like my servant Job.
9 Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
So Eliphaz the Temanite and Bildad the Shuhite [and] Zophar the Naamathite went, and did according to that which Yahweh had spoken unto them, —and Yahweh accepted Job.
10 Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
And, Yahweh himself, turned the captivity of Job, when he prayed in behalf of his friends, —and Yahweh increased all that Job had possessed, unto twice as much.
11 Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
Then came unto him all his brethren and all his sisters, and all his former acquaintances, and they did eat bread with him in his house, —and shewed sympathy with him and comforted him, over all the calamity which Yahweh had brought upon him, —and they gave him, every one a weight of money, and every one, a ring of gold.
12 Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
And, Yahweh, blessed the latter end of Job, more than his beginning, —and so he came to have fourteen thousand sheep, and six thousand camels, and a thousand yoke of oxen, and a thousand she-asses.
13 Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
And he came to have seven sons, and three daughters;
14 ’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
and he called the name of the first Jemima, and the name of the second Kezia, —and the name of the third, Keren-happuch.
15 Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
And there were found no women so fair as the daughters of Job, in all the land, —and their father gave them an inheritance, in the midst of their brethren.
16 Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
And Job lived, after this, a hundred and forty years, —and saw his sons and his sons’ sons, four generations.
17 Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.
So Job died, old and satisfied with days.