< Ayuba 42 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Then answered Job unto the Lord, and said,
2 “Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
I acknowledge that thou art able to do every thing, and that no deep plan of thine can be restrained.
3 Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
Who is he that dareth to conceal [thy] counsel without knowledge? Truly I have spoken of what I understood not, of things too wonderful for me, which I knew not.
4 “Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
Oh do but hear [me], and I will indeed speak: I will ask of thee, and do thou inform me.
5 Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
I had only heard of thee by the hearing of the ear; but now my eye hath seen thee.
6 Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
Therefore I reject [what I have said], and repent; because I am dust and ashes.
7 Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
And it came to pass, after the Lord had spoken these words unto Job, that the Lord said to Eliphaz the Themanite, My wrath is kindled against thee, and against thy two friends; because ye have not spoken of me properly, like my servant Job.
8 Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
And now take unto yourselves seven bullocks and seven rams, and go to my servant Job, and offer up a burnt-offering in your behalf; and my servant Job shall pray for you; for him alone will I receive favorably, so as not to deal with you after your folly; because ye have not spoken of me properly, like my servant Job.
9 Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
Then went Eliphaz the Themanite and Bildad the Shuchite and Zophar the Na'amathite, and did in accordance with what the Lord had spoken to them: and the Lord received Job in favor.
10 Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
And the Lord brought back the captivity of Job, when he prayed in behalf of his friends; and the Lord increased all that Job had had twofold.
11 Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
And then came unto him all his brothers, and all his sisters, and all that had been of his acquaintance before, and ate bread with him in his house; and they condoled with him, and comforted him for all the evil that the Lord had brought upon him; and they gave him, every one, a kessitah, and every one an earring of gold.
12 Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
And the Lord blessed the latter end of Job more than his beginning: and he had fourteen thousand sheep, and six thousand camels, and a thousand yoke of oxen, and a thousand she-asses.
13 Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
He had also seven sons and three daughters.
14 ’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
And he called the name of the first Jemimah; and the name of the second, Keziah; and the name of the third, Keren-happuch.
15 Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
And there were not found such handsome women as the daughters of Job in all the land; and their father gave them an inheritance among their brothers.
16 Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
And Job lived after this one hundred and forty years: and he saw his sons, and his sons' sons, even four generations.
17 Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.
Then died Job, being old and full of days.

< Ayuba 42 >